Connect with us

Labarai

Jami’an tsaro sun kama bindigogi 150 a gidan ɗan ta’adda a Neja

Published

on

Jami’an tsaro sun gano bindigogi ƙirar AK-47 kimanin 150 da albarusai sama da 3,000 a gidan wani ɗan bindiga da suke nema ruwa a jallo a jihar Neja.

Majiyoyi sun ce an yi ɗauki ba daɗi tsakanin ɗan bindigar da jami’an tsaro na tsawon sa’o’i a daren Talata, a unguwar Gbeganu da ke Minna, babban birnin jihar, inda suka gano bindigogin da harsasai sama da 3,000.

Wata majiyar tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa makaman da aka kama a gidan ɗan bindigar sun haɗa da bindigogi ƙirar AK-47 guda 150, bindiga ƙirar AA, albarusai 3,000, makamin roka, da kuma abubuwan fashewa.

Mazauna yankin sun ce sun shiga tashin hankali da jin musayawar wutar da aka fara da misalin ƙarfe 12 na dare, kafin ɗan bindigar ya tsere.

Sun bayyana cewa wanda ake zargin ya yi amfani da makamin roka ya rusa wani ɓangare na gidan nasa, inda ta nan ya samu ya tsere, amma jami’an tsaro sun kama matarsa ’ya’yansa da ke gidan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun yi artabu da gungun masu aikata laifuka, sun ƙwato bindigogin guda biyu

Majiyarmu ta ce ganin jami’an tsaro ta na’urar CCTV ke da wuya, sai ɗan ta’addan da suka je nema ya buɗe musu wuta, su kuma suka mayar da martani.

Wani mazaunin unguwar ya shaida wa wakilinmu cewa, “gaskiya ba mu yi barci ba, saboda ƙarfin ƙarar harbe-harben, yadda ka san bom ake harbawa.

“Ta ƙofar gidanmu jami’an tsaron suka wuce a lokacin da za su gidan, ba mu san inda suka nufa ba, sai daga baya muka fara jin harbe-harbe.”

Ya bayyana cewa harsashi ya samu wani mai gadi a ayin musayar wutar, inda aka kai shi Asibitin ƙwararru Ibrahim Badamasi Babangida domin ba shi kulawa.

A lokacin da wakilinmu ya je yankin a safiyar Talata, ya ga wasu bangayen gidan sun faɗi, ƙofa da bango da kuma tagogin gidan kuma da ruwan harsasai a jikinsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like