No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an tsaro a Neja sun gano bama-bamai da aka binne

Jami’an tsaro a Jihar Neja, sun gano wasu bama-bamai da abubuwan fashewa da yawa a wurare daban-daban da aka binne a wasu yankunan jihar.

Wuraren da aka binne bama-baman sun haɗa da yankin Galadima-Kogo a Ƙaramar Hukumar Shiroro, yankin Mutun-Daya a ƙaramar hukumar Munya, da yankin Gbeganu da ke Minna.

Kakakin Rundunar ’yan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun ne, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Katsina sun kama matashin da ya sare hannun ƙanin mahaifinsa

Ya bayyana cewa an gano abubuwan fashewar ne yayin ayyukan yaki da ta’addanci tsakanin shekarar 2021 zuwa 2023.

A Galadima-Kogo, wani bam ya tashi a shekarar 2022, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wasu jami’an Hukumar Sibil Difens (NSCDC).

An ɓoye abubuwan fashewar ne a wurare daban-daban, amma tawagar ‘yan sanda tare da sauran hukumomin tsaro a jihar sun gano su, inji kakakin ‘yan sandan.

Abiodun, ya ƙara da cewa an lalata bama-baman a ranar 22 ga watan Agusta, 2024, a bayan Dutsen Zuma da ke Suleja.

Ya ce aikin ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin SP Mohammed Mamun, wanda ke kula da sashen lalata bama-bamai na rundunar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...