No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto wasu mutane bakwai da suka maƙale a ƙarƙashin wata katanga da ta ruguje a dandalin Malam Ƙato da ke kusa da Shagon Sufaye a cikin birnin Kano.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Alhaji Saminu Abdullahi ya fitar ranar Lahadi a Kano.

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar.

“Mun samu ƙiran waya daga wani Malam Bashir Mansur da misalin ƙarfe 05:43 na rana cewa bango ya rushe.

KU KUMA KARANTA: Ɗaliba ta tayar da gobara a makaranta saboda an ƙwace mata waya, 19 sun mutu

“Bayan samun labarin, mun yi gaggawar aika ‘yan kwana-kwana zuwa wurin da abin ya faru da misalin ƙarfe 05:47 na yamma,” in ji shi.

Ya ce wani gefen katangar da ke dandalin Malam Ƙato ya ruguje ya kuma shafi mutane bakwai.

Ya bayyana sunayen waɗanda abin ya shafa da Abubakar Abdullahi mai shekaru 30; Abdulsalam Idris, 20,  Usman Abdullahi, 20,  Usaini Muhammed, 30, Umar Isah, 40.

Abdullahi ya ce, ‘yan kwana-kwana sun ceto dukkan waɗanda abin ya shafa da ransu, inda ya ce biyar daga cikinsu da ƙananan raunuka an kai su asibitin koyarwa na Abdullahi Wasai yayin da wasu biyu da suka samu munanan raunuka aka garzaya da su asibitin Albarka domin kula da lafiyarsu.

Ya ce ba a rasa rai ba, inda ya ƙara da cewa ana gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...