No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire (JAMB), ta biya jimillar kuɗi zunzurutu har Naira biliyan 1,478,416,000.00 ga masu shirya jarabawar JAMB, wato ‘Computer Best Test’ (CBT) a duk faɗin ƙasar nan, don ayyukan da suka yi a lokacin jarabawar gama gari ta UTME ta wannan shekarar 2023.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan hulɗa da jama’a da ƙa’ida na hukumar, Dakta Fabian Benjamin ya fitar kuma ya bayyanawa manema labarai a Abuja ranar Alhamis.

Mista Benjamin ya ce adadin bai kai miliyan 59,585,000 ba, wanda wani ɓangare ne na kuɗaɗen da aka amince da su na cibiyoyin CBT mallakar JAMB.

Ya ce ya dace kawai a gaggauta warware wajibai kamar yadda ya kamata don inganta da kuma ɗorewar kyakkyawar alaƙar aiki tare da abokan hulɗar da suka gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

KU KUMA KARANTA: Hukumar JAMB za ta karɓi ɗaliban Najeriya da suka dawo daga Sudan zuwa jami’o’in ƙasar

“A sani cewa yawancin cibiyoyin da ake amfani da su wajen jarrabawar ba na JAMB ba ne yayin da wasu kuma cibiyoyin ICT na manyan makarantun ne.

“Wannan dangantakar da ke tsakanin Hukumar da cibiyoyin CBT masu zaman kansu da sauran su na haɗin gwiwa ne a cikin yanayi kuma an tsara su don tabbatar da ingantacciyar isar da sabis da haɗa kai.

“Saboda haka, Hukumar tana alfaharin sanar da cewa duk masu cibiyoyi da suka yi aiki mai inganci a lokacin jarabawar da aka kammala an yaba musu yadda ya kamata saboda aikin da suka yi da kyau kuma sun biya daidai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, a matsayinta na ƙungiyar da ta ɗauki nauyin hukumar, za ta ci gaba da tabbatar da cewa kowane ɗan takara ya samu damar shiga manyan makarantu ba tare da wata matsala ba ta hanyar samar da daidaito ga kowa da kowa.

Don haka, ya nanata ƙudurin hukumar na ci gaba da yin amfani da fasahar zamani, ba wai kawai ta samar da ingancin tantancewa ba, har ma da kare martabar jarabawar ta.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

4 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...