No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta tabbatar da cewa mutane biyar sun samu raunuka daban-daban a wani hari da mayaƙan Boko Haram suka haɗa kai a ƙaramar hukumar Gwoza da ke jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abdu Umar ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Asabar a Maiduguri.

Ya ce ‘yan ta’addan sun yi harbin bindiga da dama a kan masu kaɗa ƙuri’a daga kololuwar tsaunin Mandara, inda ya ce mutane biyar sun samu raunuka a harin. Umar ya ce waɗanda abin ya shafa sun haɗa da mata biyu da maza uku.

“Ƙoƙarin da sojoji suka yi a yankin ya taimaka wajen fatattakar ‘yan ta’addar, wanda ya tilasta musu gudu saboda ƙarfin harsashi” in ji shi.

CP ya ce tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya yayin da ake ci gaba da kaɗa ƙuri’a. An miƙa waɗanda abin ya shafa asibiti domin yi musu magani.

KU KUMA KARANTA: Kuɗi shine mabuɗin shirye-shiryen gudanar da aiki a ranar zaɓe – Jega

A halin da ake ciki, ƙungiyar farar hula a Borno (NECSOB) ta bayyana ƙwarin guiwar yadda masu kaɗa ƙuri’a suka fito a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya a jihar.

Shugaban ƙungiyar, Mista Bulama Abiso, wanda ya jagoranci tawagar masu sa ido a zaɓen, ya bayyana fitowar zaɓen a matsayin abin ƙarfafa gwiwa.

Sai dai ya lura cewa akwai jinkiri na Bimodal Accreditation System (BVAS) wanda ya haifar da tsaiko a farkon fara kaɗa kuri’a.

Abiso ya buƙaci masu kaɗa ƙuri’a da su riƙa gudanar da ayyukansu cikin tsari domin sauƙaƙa gudanar da aikin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...