Connect with us

Laifi

Jama’a sun jikkata biyo bayan hari ranar zaɓe, a Borno

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta tabbatar da cewa mutane biyar sun samu raunuka daban-daban a wani hari da mayaƙan Boko Haram suka haɗa kai a ƙaramar hukumar Gwoza da ke jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abdu Umar ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Asabar a Maiduguri.

Ya ce ‘yan ta’addan sun yi harbin bindiga da dama a kan masu kaɗa ƙuri’a daga kololuwar tsaunin Mandara, inda ya ce mutane biyar sun samu raunuka a harin. Umar ya ce waɗanda abin ya shafa sun haɗa da mata biyu da maza uku.

“Ƙoƙarin da sojoji suka yi a yankin ya taimaka wajen fatattakar ‘yan ta’addar, wanda ya tilasta musu gudu saboda ƙarfin harsashi” in ji shi.

CP ya ce tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya yayin da ake ci gaba da kaɗa ƙuri’a. An miƙa waɗanda abin ya shafa asibiti domin yi musu magani.

KU KUMA KARANTA: Kuɗi shine mabuɗin shirye-shiryen gudanar da aiki a ranar zaɓe – Jega

A halin da ake ciki, ƙungiyar farar hula a Borno (NECSOB) ta bayyana ƙwarin guiwar yadda masu kaɗa ƙuri’a suka fito a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya a jihar.

Shugaban ƙungiyar, Mista Bulama Abiso, wanda ya jagoranci tawagar masu sa ido a zaɓen, ya bayyana fitowar zaɓen a matsayin abin ƙarfafa gwiwa.

Sai dai ya lura cewa akwai jinkiri na Bimodal Accreditation System (BVAS) wanda ya haifar da tsaiko a farkon fara kaɗa kuri’a.

Abiso ya buƙaci masu kaɗa ƙuri’a da su riƙa gudanar da ayyukansu cikin tsari domin sauƙaƙa gudanar da aikin.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Atiku ya lashe zaɓe a mazaɓar Ahmed Lawan, a Yobe | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Atiku ya lashe zaɓe a mazaɓar elRufa’i da ta Ahmed Lawan - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Laifi

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Published

on

'Yan bindiga sun sace 'yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Daga Idris Umar, Zariya

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ‘yan jarida biyu a ƙauyen Danhonu da ke ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kai hari a cikin al’umma a daren ranar Asabar inda suka yi awon gaba da ‘yan jarida biyu da iyalansu.

Waɗanda abin ya shafa, Alhaji AbdulGafar Alabelewe da AbdulRaheem Aodu, ‘yan jarida ne na jaridun The Nation da Blueprint a jihar Kaduna, bi da bi.

Alabelewe wanda shi ne shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), majalisar jihar Kaduna a halin yanzu, an dauke shi tare da matarsa da ‘ya’yansa biyu.

An kuma yi garkuwa da Aodu da matarsa, inda suka bar ‘yarsu da ba ta da lafiya.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

Da yake bayyana hakan, Taofeeq Olayemi, dan uwa na daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya ce ‘yan bindigar sun afkawa al’ummar ne da misalin karfe 10:30 na dare, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su yi awon gaba da su.

Da farko ‘yan fashin sun tafi da Alabelewe, matarsa, ‘ya’yansa uku, da kuma wani bako, amma daga baya suka sako yarinyar daya daga cikin yaran.

“Sun shiga gidan Abdulgafar ta katanga.

“Sun shiga cikin ɗakin kwanansa kai tsaye suka ɗauko shi da matarsa da ‘ya’yansu biyu suka tafi nan take, inda ‘yan banga suka iso suka fara harbin iska,”

Ya zuwa haɗa wannan rahoton babu ɗuriyar duk wanɗana aka sacen.

Tuni kunyar ‘yan jaridar ta jihar Kaduna ta sanar tare da tabbatar da faruwar lamarin.

Continue Reading

Laifi

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Published

on

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Ana zargin wani matashi mai suna Ufuoama Umurie ya kashe mahaifinsa a Unguwar Okpare da ke Ƙaramar Hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, ranar Laraba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, an tsinci gawar mahaifin mai suna Rabaran Isaac Umurie, wanda ɗaya ne daga cikin limaman cocin St. John’s Anglican da ke Okpare-Olomu a safiyar wannan Larabar.

Bayanai sun ce tun farko lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar dare, inda wanda ake zargin ya kori mahaifiyarsa a lokacin da take ƙoƙarin ceto rayuwar mijinta amma ita kanta da ƙyar ta tsira.

Ufuoma, wanda a halin yanzu yana hannun ‘yan sanda, an ce ya yi amfani da laujen yankar ciyawa ya yanka mahaifinsa sannan ya sassare shi a sassan jikinsa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni sun ce matashin ya yi wa mahaifinsa wannan aika-aikar ce a lokacin da yake barci kafin maƙwabta da mabiya cocin su su kawo ɗauki.

Duk da cewa har yanzu ba a gano abin da ya haddasa faruwar lamarin ba, wasu mazauna unguwar yankin sun yi zargin cewa Ufuoma yana fama da taɓin hankali, kuma wannan ne karo na biyu da ya kai wa mahaifin nasa hari.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like