No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jakadiyar Isra’ila a Birtaniya ta yi watsi da yiwuwar samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kansu a matsayin hanyar warware rikicin da ya biyo bayan mamayar da Isra’ila ta yi wa yankunan Falasɗinawa na tsawon shekaru, a wata hira da ta yi da gidan talabijin na Sky News.

“Ina ganin lokaci ya yi da duniya za ta fahimci tsarin Oslo ya gaza a ranar 7 ga watan Oktoba, kuma muna buƙatar sake gina wani sabon tsari,” in ji Tzipi Hotovely, yayin da take magana kan ranar da ƙungiyar gwagwarmayar Falasɗinawa ta Hamas ta ƙaddamar da wani harin ba-zata a Isra’ila.

Ta ƙara da cewa “Isra’ila ta sani a yau kuma ya kamata duniya ta sani cewa yarjejeniyar Oslo ta gaza saboda Falasɗinawa ba su taɓa son samun ƙasa kusa da Isra’ila ba, suna son samun ƙasa tun daga kogi har zuwa teku.”

KU KUMA KARANTA: An kai wa jirgin ruwa hari a Bahar Maliya yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a Gaza

Hotovely ta tambayi ɗan jaridar Mark Austin, dalilin da ya sa ya damu da batun tsarin samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kansu, bayan da ya tambaye ta ko wannan yunƙurin ya mutu ne.

Da aka tambayi ra’ayinta game da kalaman shugaban Amurka Joe Biden na cewa Isra’ila tana “rasa goyon baya” kan harin bama-bamai da take kaiwa Gaza, sai ta ce “Amurkawa suna yaƙar ISIS [Daesh] a Mosul, [Iraƙi], akwai mutanen da aka kashe a Mosul daidai ko fiye da na Gaza.”

Hotovely ta yi iƙirarin ƙarya cewa Isra’ila “tana yin duk abin da zai hana asarar rayuka” kuma ta ce makarantun Majalisar Ɗinkin Duniya a Gaza “sun zama makarantun ta’addanci.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...