No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce Tel Aviv a shirye take ta “zafafa” hare-haren da take kaiwa Gaza idan aka gaza cimma nasarar amincewa da sakin mutanen da Hamas ke garkuwa da su a yankin Falasɗinu, a tattaunawar sulhu da ake yi a Masar.

Gallant ya ce Isra’ila ta shirya tsaf domin ganin ta kuɓutar da mutanen da ake garkuwa da su a Gaza, in ji Gallant bayan da ya zagaya yankin Rafah biyo bayan kutsen da Isra’ila ta yi a kan iyakar Rafah da ke kudancin yankin.

Amma “idan aka cire wannan batun a tattaunawar, to mu ci gaba da zafafa hare-haren,” in ji shi a cikin wata sanarwa.

KU KUMA KARANTA: Tankokin yaƙin Isra’ila sun shiga kudancin birnin Rafah na Gaza — Rahoto

Kalaman Gallant na zuwa ne bayan da masu shiga tsakani na Isra’ila suka isa birnin Alkahira domin yin wani yunƙuri na baya-bayan nan na sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma tsagaita wuta a yaƙin da Isra’ila ta kwashe watanni bakwai tana yi a Gaza.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...