No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ila ta yi watsi da ƙudirin da Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya wanda ya amince a “tsagaita wuta” a Gaza.

A wata sanarwa da jaridar Haaretz ta wallafa, ta ambato ma’aikatar tana cewa “babu wata kafa ta tsagaita buɗe wuta” muddin ƙungiyar Hamas ta Falasɗinawa ta ci gaba da rike mutanen da ta yi garkuwa da su.

Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ranar Laraba ya amince da wani daftari wanda ya yi ƙira a “gaggauta tsagaita wuta” a faɗin Gaza.

Kasashe goma sha biyu ne suka amince da ƙudurin wanda ƙasar Malta ta gabatar, yayin da Amurka da Birtaniya da Rasha suka ƙaurace wa kaɗa ƙuri’a.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...