No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an kiwon lafiya na Gaza sun bayyana cewa da sanyin safiyar yau Talata ne aka kashe Falasɗinawa 20 a hare-haren da Isra’ila ta kai a Rafah da wasu yankuna a tsakiyar Gaza.

Jami’an kiwon lafiya na Gaza sun ce mutum 14 ne suka mutu kana wasu da dama suka jikkata, sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai kan gidaje da gidaje da dama a birnin Rafah da ke kudancin Gaza a kusa da kan iyakar Masar, inda Falasɗinawa sama da miliyan ɗaya suke samun mafaka,.

Wasu karin mutum shida sun mutu a wani harin da aka kai ta sama a wani gida a sansanin Al-Nuseirat da ke tsakiyar Gaza, in ji su.

A Deir al Balah, wani gari da ke tsakiyar Gaza mai tazarar kilomita 14 kudu da birnin Gaza, ƙarar fashe-fashe da suka haɗe da tsawa, da ruwan sama sun ƙara jefa iyalan da suka rasa matsugunansu a sansanonin cikin tashin hankali da fargaba.

KU KUMA KARANTA: Sama da yara 13,000 Isra’ila ta kashe a Gaza – UNICEF

“Ba za mu iya bambance tsakanin sautin tsawa da tashin bama-bamai ba,” in ji Shaban Abdel-Raouf, mahaifin ‘ya’ya biyar, ta wata manhajar tattaunawa.

“Mun kasance a da muna jiran damina muna roƙon Allah ya kawo ta da wuri. Amma a yau muna addu’ar kada a yi ruwa, mutanen da suka rasa matsugunansu suna cikin matuƙar wahala,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...