Isra’ila ta kutsa kai cikin sansanonin Falasɗinawa, inda rikici ya ɓarke

0
58
Isra'ila ta kutsa kai cikin sansanonin Falasɗinawa, inda rikici ya ɓarke

Isra’ila ta kutsa kai cikin sansanonin Falasɗinawa, inda rikici ya ɓarke

Sojojin Isra’ila sun kai farmaki a garin Tulkarem da sansanin ‘yan gudun hijira na Balata da ke arewacin Gabar Yammacin Kogin Jordan.

Dakarun mamaya na Isra’ila sun mamaye Tulkarem bayan tsakar dare, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Falasɗinawa Wafa ya bayyana.

Rahoton ya ƙara da cewa, wasu motocin sojojin mamaya tare da rakiyar manyan buldoza guda biyu sun shiga birnin daga ɓangarensa na yammacin ƙasar, inda suka fara rusa ababen more rayuwa a yankin Al-Alemi, yayin da wani jirgin sama mara matuƙi na sa ido ya yi ta shawagi ta saman birnin.

Wafa ya kuma ruwaito cewa, sojojin Isra’ila sun kai farmaki sansanin ‘yan gudun hijira na Balata da ke gabashin Nablus tare da rakiyar buldoza ta soji, lamarin da ya kai ga arangama da dakarun gwagwarmayar Falasɗinawa.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa da dama a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan

Shaidun gani da ido sun ce an yi arangama tsakanin Falasɗinawa da sojoji a kofar shiga sansanin.

Masu fafutuka sun yaɗa bidiyon da ke nuna motocin soji da kuma buldoza yayin farmakin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here