Isra’ila ta kashe ‘yan gudun hijira 90 a wani sansani da ke Gaza

0
171

Isra’ila ta ƙaddamar da munanan hare-hare a Gaza, inda ta kai hari a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke arewacin birnin, da kuma asibiti a kudanci inda sojojin suka kashe wata matashiya wadda ta rasa kafarta a wani hari na baya da suka kai, kamar yadda hukumomin Falasɗinu suka shaida.

Harin da Isra’ila ta kai sansanin ‘yan gudun hijira na Jabalia da ke arewacin Gaza ya yi sanadin mutuwar Falasɗinawa 90, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar lafiya ta Gaza ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

KU KUMA KARANTA: Hezbollah ta ce ta halaka sojojin Isra’ila da dama a wani hari kan sansaninsu

Wani makami mai linzami da aka harba a gidan iyalan Shehab ya yi sanadin mutuwar mutum 24, kamar yadda gidan rediyon Aqsa na Hamas ya sanar.

Leave a Reply