Isra’ila ta kashe gomman Falasɗinawa a ranar farko ta Azumin Ramadana

An kashe gomman Falasɗinawa an raunata da dama a wani hari da Isra’ila ta kai a Gaza a rana ta farko ta Azumin Ramadana a ranar Litinin, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Falasɗinu wato WAFA ya ruwaito.

Rahotanni sun ce jirgin yaƙin Isra’ila ya kashe mutane a dama a unguwannin Zaytoun da Sabra da kuma birnin Khan Younis da ke kudancin Zirin Gaza.

Haka kuma sojojin na Isra’ila sun ƙona wata gona a unguwar Salam wadda ke a birnin Rafah.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *