Connect with us

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Published

on

Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa aƙalla 29 a harin da ta kai ta sama a wata makaranta da ‘yan gudun hijira suke samun mafaka a kudancin Gaza ranar Talata, a yayin da luguden wutar da dakatunta suke ci gaba yi a arewaci ya sa aka rufe asibitocin Birnin Gaza tare da tilasta wa mutane tserewa daga gidajensu domin neman mafaka.

Sojojin Isra’ila sun yi kisan kiyashi a makarantar Al-Awda da ke garin Abasan na gabashin Khan Younis, a cewar wata sanarwa da Ma’aikatar Kiwon Lafiya ta Gaza ta fitar.

Galibin yankunan Birnin Gaza sun kasance tamkar kufayi sakamakon luguden wutar da dakarun Isra’ila suka kwashe watanni tara suna yi a yankin. Yawancin mutanen da ke birnin sun tsere tun da aka fara yaƙin, amma dubban mutane na ci gaba da zama a arewaci.

KU KUMA KARANTA: An yi zanga-zangar neman ƙasashen Musulmai su tura sojoji don taimaka wa Falasɗinawa a Gaza

A watanni tara da Isra’ila ta kwashe tana yaƙi a Gaza, dakarunta sun mamaye asibitoci aƙalla takwas, inda suka kashe majinyata da ma’aikatan kiwon lafiya tare da lalata gine-gine da kayan aiki.

Isra’ila ta yi zargin cewa ƙungiyar Hamas tana mafani da asibitocin ne domin ajiye makamai, ko da yake ba ta bayar da cikakkun shaidu game da zargin nata ba.

Asibitoci 13 daga cikin 36 da ke Gaza ne suke aiki a halin yanzu, kuma su ɗin ba ba sa aiki kamar yadda ya kamata, a cewar ofishin jinƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu – MƊD

Published

on

Isra'ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu - MƊD

Isra’ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu – MƊD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana girman mamayar da sojojin Isra’ila suke yi wa yankin Gaza, tana mai cewa an kori kusan kashi 84 daga yankin.

Da yake bayani kan alƙaluman da Ofishin Babban Mai Kula da Harkokin Jinƙai na Majalisar (OCHA) ya tattara, mataimakin kakakin ofishin Farhan Haq ya shaida wa manema labarai cewa “luguden wuta da kuma kutsen da Isra’ila take yi a Gaza na ci gaba da kashewa da jikkatawa tare da korar Falasɗinawa daga matsugunansu, da kuma rusa gidajensu da sauran gine-gine da suka dogara a kansu.”

Ya ce, “Sau biyu sojoji suna bayar da umarni ga mutane su fita daga Khan Younis a ƙarshen mako, zuwa yankunan da a baya galibi aka umarci mutane su fice daga cikinsu.”

KU KUMA KARANTA: Dubban Falasɗinawa sun tsere daga wani yanki a tsakiyar Gaza

Wannan lamari ya shafi yankuna 23 da wurare 14 da ke samar da ruwa da tsaftar jama’a da kuma makarantu huɗu.

“Jimilla, sojojin Isra’ila sun kori mutane daga wurin da ya kai girman murabba’in kilomita 305, wato kusan kashi 84 na yankin Zirin Gaza,” in ji shi.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

Published

on

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

Jamhuriyar Dimukuraɗiyyar Congo ta ce ta fara tattaunawa da Zambia kwana guda bayan da maƙociyarta ta kudancin Afirka ta rufe iyakarsu.

Matakin ya toshe babbar hanyar da Congo ke amfani da ita don fitar da Copper zuwa ƙasashen waje, a matsayinta na ƙasa ta biyu a duniya a yawan fitar da ƙarfen Copper.

A ranar asabar, ministan kasuwanci na Zambia, Chipoka Mulenga ya sanar da rufe iyakar na wani ɗan lokaci, bayan Congo ta saka haramcin amfani da lemon zaƙi da barasa da aka shigo da ita, inda ya haifar da zanga-zangar direbobin dakon kaya a garin Kasumbalesa da ke iyakar Zambia.

KU KUMA KARANTA: Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

“An fara tattaunawa tsakanin gwamnatocin Congo da Zambia tun ranar Lahadin nan, don hanzarta sake buɗe ƙofar iyakar tasu,” in ji wata sanarwa da Ma’aikatar Kasuwanci ta Congo ta fitar a ranar Lahadi.

“A awannin da suka biyo baya, ɓangarorin biyu za su haɗu a Lubumbashi da ke Haut-Katanga, don nemo mafita ta ƙarshe game da kasuwancin.”

Ministan Kasuwanci na Congo, Julien Paluku Kahongya, ya fitar da sanarwa a ranar Lahadi, inda yake cewa ma’aikatarsa ta samu sanarwa a hukumance game da taƙaddamar kasuwanci daga Zambia kafin ta sanar da rufe iyakar.

A sanarwar, ya yi dogon bayani game da yarjejeniyar kasuwancin ƙasashen biyu da kuma hanyoyin magance duk wata taƙaddama da ta taso.

“Ya zuwa yanzu babu wata taƙaddama da aka gabatar wa ma’aikatar a rubuce, ko ta hanyar diflomasiyya,” in ji shi. “Ma’aikatar ta shirya duba duk wata buƙata da Zambia ta kawo, matuƙar tana ƙunshe cikin yarjejeniyar, wadda ta hana ramuwar gayya.”

Congo ce ƙasa ta biyu a duniya a fannin samar da ƙarfen Copper, kuma ta zo ta 3 a 2023 wajen fitar da shi, bayan ta fitar da tan miliyan 2.84.

Zambia hanya ce mai muhimmanci ga Congo, wajen fitar da Copper, inda ake bi ta garin Kasumbalesa a shiga Zambia.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An soke wasannin da Taylor Swift za ta yi i a Austria

Published

on

An soke wasannin da Taylor Swift za ta yi i a Austria

An soke wasannin da Taylor Swift za ta yi i a Austria

Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ruwaito cewa da yawa daga cikin masoyan nata sun kashe dubban kuɗaɗen Euro wajen yin tafiya da kama otel da kuma abinci.

Masoyan Taylor Swift sun nuna rashin jin daɗinsu bayan da aka soke wasannin da mawaƙiyar za ta yi guda uku waɗanda tuni an kammala sayar da tikitinsu a Austria.

Soke wasannin ya biyo bayan bayanan sirri da hukumomin tsaro suka ce sun gano waɗanda ke cewa akwai a kai harin ta’addanci a birnin Vienna.

Da yawa daga cikin masoyanta sun ɗunguma zuwa shafukan sada zumunta don nuna rashin jin daɗinsu kan soke wasannin mawaƙiyar ta Amurka ‘yar asalin jihar Pennsylvania.

KU KUMA KARANTA;Ruwan sama ya lalata gidaje da dama a garin Faguji, jihar Bauchi

Wasu masoyan nata sun bayyana yadda suka kwashe watanni suna shirin halartar wasannin har ma suka ware wasu kaya na musamman da za su saka a lokacin.

Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ruwaito cewa da yawa daga cikin masoyan nata sun kashe dubban kuɗaɗen Euro wajen yin tafiya da kama otel da kuma abinci.

Hukumomi sun ce sun kama mutum biyu masu tsatstsauran ra’ayi, inda ɗayansu ya amsa yin mubaya’a ga ƙungiyar IS mai iƙirarin jihadi.

Continue Reading

You May Like