Isra’ila ta kama wata babbar ‘yar siyasar Falasɗinu

0
157

Isra’ila a ranar Talata ta kama wata babbar ‘yar siyasar Falasdinu Khalida Jarrar daga gidanta da ke Gabar Yamma da Kogin Jordan.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa dakarun na Isra’ila sun kai samame birnin Al-Bireh tare da kama Jarrar bayan gudanar da bincike a gidanta.

Isra’ila ta sha kama ta, inda lokaci na ƙarshe da aka sake ta shi ne Satumbar 2021 bayan ta shafe shekara biyu a tsare.

Leave a Reply