No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sanarwar tasa na zuwa ne bayan da shugaban Amurka Joe Biden ya caccaki yadda Isra’ila ke ci gaba da luguden wuta ba kakkautawa a kan Zirin Gaza, a matsayin martani ga harin ranar 7 ga watan Oktoba  da Hamas ta kai mata.

A ranar laraba ƙawayen Isra’ila sun zafafa matsin lamba a kanta sakamakon wannan yaƙin da ta ke yi da Hamas, inda ma Amurka da kanta ta bayyana hare-haren a matsayin na kan mai-uwa-da-wabi.

Ko a ranar talata sai da babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya ya amince da wani kudiri na neman tsagaita wuta, lamarin da ya ta’azzara matsin lamba a kan Isra’ila da Amurka.

KU KUMA KARANTA: Jakadiyar Isra’ila a Birtaniya ta ƙi amincewa da samar da ƙasashe biyu a matsayin mafita ga yakin Gaza

Ya zuwa yanzu adadin waɗanda suka mutu a wannan hare-haren da Isra’ila ke kai wa Zirin Gaza tun bayan harin 7 ga watan Oktoba ya zarce dubu 18, kuma har yanzu tana ci gaba da hare-hare, duk da buƙatar Amurka ta sara ana duban bakin gatari.

Mahukuntan yankin Falasɗinu sun ce samamen da Isra’ila ta fara a garin Jenin tun a ranar Talata da ta gabata ya yi sanadin mutuwar Falasɗinawa 10.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...