No menu items!

Sample Page Title

Date:

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce Isra’ila ta fitar da wani sabon wa’adi, inda ta umarci mazauna yankunan babban birnin Gaza da aka yi wa ƙawanya da su gudu.

Ofishin kula da ayyukan jinƙai na MƊD, OCHA, ya ce Isra’ila ta fitar da taswirori da ke nuna sabbin wuraren da suka shafi kusan kashi 20 cikin 100 na birnin Khan Younis da aka yi wa ‘yan gudun hijira.

Kafin faɗan ya ɓarke, yankin na da mutane sama da 110,000, in ji OCHA.

Ya kuma ƙara da cewa yankin ya haɗa da matsuguni 32 da ke ɗauke da ‘yan gudun hijira sama da 140,000, waɗanda akasarin su a baya sun yi gudun hijira daga arewa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...