No menu items!

Sample Page Title

Date:

Isra’ila ta ƙaddamar da wani hari a tsakiyar Beirut

Dakarun Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare ta sama da sanyin safiyar Litinin a yankin Kola na birnin Beirut, wanda ya kasance irinsa na farko da suka kai a cikin babban birnin na Lebanon tun da suka soma yaƙi da Hezbollah a watan Oktoban da ya wuce.

Wani wakilin kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya ruwaito cewa jirgi mara matuƙi na Isra’ila ya kai hari a hawa na biyar na wani gida a kan hanyar da ta haɗa Beirut da Filin Jirin Saman Ƙasa da Ƙasa na Rafik Hariri.

KU KUMA KARANTA: Ba za mu bari Isra’ila ta kori Falasɗinawa ba – Sarkin Jordan 

Harin ya tayar da gobara a gidan, ko da yake ‘yan kwana-kwana sun kashe ta.

Daga bisani ƙungiyar Popular Front for the Liberation of Palestine (PFLP) ta tabbatar da cewa harin ya kashe shugabanninta uku: Mohammed Abdel Aal, wani mamba na ɓangaren siyasarta kuma shugaban sashen soja da tsaro; Imad Ouda, kwamanda soji na Lebanon, da Abdel Rahman Abdel Aal, wanda ba a bayyana matsayinsa ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...