No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban mulkin sojin Chadi Mahamat Idriss Deby Itno, wanda ya hau kan mulki bayan mutuwar mahaifinsa a 2021, ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen da za a yi a watan Mayu mai zuwa.

Mahamat Idriss Deby ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya ranar Asabar a N’Djamena, babban birnin ƙasar.

“Ni, Mahamat Idriss Deby Itno, ne ɗan takarar shugaban ƙasa na gamayyar jam’iyyun United Chad coalition a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2024,” in ji shi.

Hukumar zaɓen ƙasar ta ce za a gudanar da zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa ranar 6 ga watan Mayu mai zuwa.

KU KUMA KARANTA: Ƙasar Chadi ta sanar da ranar zaɓe don komawa tafarkin Dimokuraɗiyya

A tsakiyar watan Janairun da ya gabata, jam’iyyar Patriotic Salvation Movement (MPS) ta ayyana Mahamat Deby Itno a matsayin ɗan takararta a zaɓen shugaban ƙasa.

Deby Itno ya hau kan mulki ne a shekarar 2021 bayan mahaifinsa Idriss Deby Itno, wanda ya kwashe kusan shekara talatin a kan mulki, ya mutu a fagen yaƙi yayin fafatawa da wasu ƴan tawayen ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...