Connect with us

Labarai

Hukumar NYSC ta haɗa kai da jami’an tsaro domin ƙubutar da ‘yan hidimar ƙasa da aka sace a Zamfara

Published

on

Hukumar NYSC ta ce tana aiki tare da jami’an tsaro domin ganin an sako wasu ‘yan masu yi wa ƙasa hidima guda takwas, waɗanda aka yi garkuwa da su a Zamfara a kan hanyarsu ta zuwa sansanin horon da su da ke Sakkwato.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na NYSC, Eddy Megwa, ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya labarta cewa, ya naƙalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na NYSC babban daraktan hukumar NYSC Yusha’u Ahmed ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja, yayin wani zaman tattaunawa da mambobin kwamitin majalisar wakilai kan matasa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan Bindiga a Zamfara, sun buƙaci miliyan huɗu ga ‘yar NYSC da suka sace

Sanarwar ta ce, hukumar gudanarwar shirin tana tattaunawa da masu ruwa da tsaki daban-daban da suka haɗa da gwamnatin Zamfara, sarakunan gargajiya, malamai da dai sauransu, domin ganin an sako mutanen da aka sace ba tare da wani rauni ba.

Birgediya-janar Ahmed, ya kuma gabatar da cikakken rahoto mai ɗauke da shaida na hoto na ziyarar da ya kai ga masu ruwa da tsaki a Zamfara, lamarin da ke nuni da cewa shirin ya ba da fifiko kan tsaro da jin daɗin dukkanin jami’an ƙungiyar.

Shugaban Kwamitin Matasa na Majalisar, Martin Esin, a nasa jawabin, ya yaba wa DG bisa girmama gayyatar kwamitin da kuma irin namijin ƙoƙarin da ya yi na ganin ‘yan ƙungiyar da aka sace sun samu ‘yanci.

Mista Esin ya yi alƙawarin goyon bayan kwamitin kan duk wani lamari na majalisa da zai ba da damar shirin ya ƙarfafa kan nasarorin da ya samu a lokacin jubili.

Ya kuma yaba wa Ahmed bisa ƙoƙarin da shirin ya yi na sake buɗe sansanin ‘yan hidimar ƙasa na jihar Borno bayan an daɗe da rufe shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like