Connect with us

Labarai

Hukumar NYSC ta biya diyya ga dangin ɗan bautar ƙasa da ya ɓata

Published

on

Hukumar kula matasa masu yiwa ƙasa hidima (NYSC) ta biya kuɗin inshora ga dangin wani ɗan bautar ƙasa mai suna Omale Victor mai lambar jihar EB/21A/1487, wanda ya ɓace a shekarar 2021, a lokacin da ya yi aiki hidimar ƙasa a jihar Ebonyi.

Victor, mai shekaru 24 a lokacin, an bayyana ɓacewarsa ne a ranar 9 ga watan Nuwamban 2021, ta hannun mai ɗakinsa Innocent Ujah, wanda ya kai rahoto ga ‘yan sanda cewa Victor ya bar gidansa da misalin ƙarfe 6 na yammacin wannan rana, kuma bai dawo ba.

Kafin batarsa, Victor yana aiki ne a hukumar kula da karatun jama’a ta jihar Ebonyi dake kan tsohuwar titin Enugu/Abakaliki ta cocin Presbyterian Church Kpirikpiri, Abakaliki, a babban birnin jihar.

KU KUMA KARANTA: Masu garkuwa sun kashe ɗan bautar ƙasa, bayan karɓar kuɗin fansa

Darakta-Janar na NYSC na lokacin da sauran jami’an hukumar sun ziyarci iyalan Omale a Lokoja a shekarar 2021 lokacin da lamarin ya faru.

Tuni dai iyalan suka tuntuɓi mahukuntan hukumar NYSC.

Shugaban masu yi wa kasa hidima, NYSC, Birgediya Janar Ahmed, a lokacin da yake mika cekin kuɗin ga iyayen marigayin, Mista Samuel da Mrs Elizabeth Omale a gidansu da ke Lokoja, a ranar Alhamis, ya ce shirin zai ci gaba da tantance dangin.

Ya kuma ja hankalin ‘yan uwa da kar su yi rauni da imani da Allah, ya ƙara da cewa hukumar NYSC za ta ci gaba da nuna ƙauna da jajircewa a gare su.

Dangin Omale sun godewa hukumar NYSC bisa yadda suka kyautata ma iyalansa tun faruwar lamarin, sun kuma yi addu’ar Allah ya dawo da dansu da ransa.

Shugaban ya samu rakiyar Daraktan ayyuka na musamman Alhaji Musa Abubakar; Daraktan yaɗa labarai da hulda da jama’a Mista Eddy Megwa; Darakta, Sabis na Kula da Lafiya; Mista Ayodele Omotade; da kuma Kodinetan NYSC na jihar Kogi, Mrs Mofoluwaso Williams.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like