Hukumar NSCDC ta tura jami’ai 422 don sanya ido kan UTME a Kano

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC ko civil defence a jihar Kano, ta tura jami’ai 422 zuwa cibiyoyi 37 da aka ware na jarrabawar shiga manyan jami’o’i, UTME, da ke jihar. Kwamandan jihar, Adamu Salihu, ya bayyana haka a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Kano ranar Laraba.

Ya bayyana cewa an tura jami’an ne wuraren da ake gudanar da jarabawar domin sanya ido kan aikin da kuma samar da tsaro a wuraren da aka keɓe.

A cewarsa, rundunar ta tura jami’anta biyu zuwa kowace cibiyoyi 37 da ke faɗin jihar domin tabbatar da an gudanar da jarabawar ba tare da tangarɗa ba.

“Za a yi zaman jarabawa uku na tsawon kwanaki uku kuma a kowane zama mun tura jami’ai biyu don sanya ido kan aikin.”

KU KUMA KARANTA: JAMB ta tsayar da ranar rubuta jarabawar UTME

Malam Salihu ya ce rundunar ba ta samu wani rahoto marar kyau ba kawo yanzu. A cewarsa, jarabawar ya zuwa yanzu babu wani cikas; babu wani lamari na kuskuren jarrabawa, kuma yanayin yana da kyau.

Wakilin NAN, wanda ya ziyarci wasu cibiyoyi, ya lura cewa an fara rajistar ‘yan takara da wuri tare da samun gogewa daban-daban a yayin gudanar da aikin.

Wani mai kula da cibiyar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce an magance wasu matsalolin nan take. Ya bayyana cewa har yanzu jarabawar ba su da matsala.

NAN ta ruwaito cewa ana sa ran ‘yan takara miliyan 1.5 za su rubuta jarabawar a faɗin ƙasar, ta hanyar amfani da jimillar cibiyoyi 740 don gwajin Kwamfuta, CBT.


Comments

One response to “Hukumar NSCDC ta tura jami’ai 422 don sanya ido kan UTME a Kano”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Hukumar NSCDC ta tura jami’ai 422 don sanya ido kan UTME a Kano […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *