Connect with us

Labarai

Hukumar NSCDC a Gombe ta kama mutane takwas kan zargin sayar da naman mushe

Published

on

Hukumar tsaro ta ‘Nigerian Security and Civil Defence Corp’ (NSCDC) a jihar Gombe ta gabatar da wasu mutane takwas da ta kamo da ake zargin suna sayar wa mutane mushen nama.

Da yake gabatar da waɗanda ake zargin ga manema labarai a hedkwatar hukumar, Kwamandanta na Jihar Gombe, Muhammad Bello Mu’azu, ya ce rundunar ta fara kama jagorar waɗanda ake zargin ce mai suna Mary Paul tare wasu mutum huɗu, kafin daga bisani ta sake kama wasu ƙarin mutum uku.

Kwamandan wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SC Buhari Sa’ad, ya yi magana a madadinsa ya ce sun kama mutanen ne bisa bayanan sirri da suka samu kan haramtacciyar sana’ar da ake zargin mutanen na yi.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NSCDC ta nemi haɗin kan ‘yan sanda akan rashin tsaro a Abuja

Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a wata kasuwar da ke a kwaryar cikin Gombe, kasancewar sun saba sayar da mushen ga jama’a a jihar da ma wasu jihohin Kudancin ƙasar nan, musamman Jihar Delta.

A cewar Kwamandan, Mary da tawagarta yawanci suna sarrafa naman ne tare da gyara shi don sayarwa jama’a ba tare da sun san naman mushe ba ne.

Ya kuma ce jami’ansa sun kama wasu ma a babur mai ƙafa uku ɗauke da wata matacciyar saniya da suka sayo daga Kanawa a yankin Ƙaramar hukumar Yamaltu Deba inda suka sa aka binne ta a wajen gari.

Muhammad Bello Mu’azu, yace da zarar sun kammala bincike za su gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu.

Sannan sai ya ƙirayi jama’a da su yi hattara da irin naman da suke saya, da inda suke saya da kuma wurin waɗanda suke saya.

Jagorar waɗanda ake zargin, Mary Paul, ta ce a baya tana sayar da naman daji ne da aka farauto, amma dai daga baya ta koma sayar da mushen.

Mary ta ce ta shafe tsawon shekaru tana wannan sana’ar inda take amfani da sinadarai wajen sarrafa naman da kuma adana shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like