No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar NiMet ta yi hasashen ruwan sama da tsawa na kwanaki 3

Hukumar kula da yanayin samaniya ta Najeriya, NiMet, ta yi hasashen yanayi na tsawa da ruwan sama daga ranar Talata zuwa Alhamis a faɗin ƙasar.

An fitar da hasashen ne a ranar Litinin a Abuja, inda hasashen ya nuna yanayin tsawa a sassan jihohin Bauchi, Kebbi, Taraba, Kano, Katsina, Adamawa, da Kaduna a safiyar ranar Talata.

A cewar hukumar, ana sa ran za a yi tsawa a duk faɗin yankin a cikin wannan ranar.

“A yankin Arewa ta tsakiya, ana sa ran tsawa a sassan jihohin Kogi, Benuwe, Filato, Babban Birnin Tarayya Abuja, Nasarawa da Neja da safe.”

KU KUMA KARANTA: Ruwan sama a Nijar ya rusa masallaci mai ɗimbin tarihi

Hukumar ta yi hasashen tsawa a sassan jihohin Taraba, Adamawa, Sokoto, Kebbi, Zamfara, Katsina, Kano da Kaduna a safiyar Laraba.

A cewar NiMet, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Borno, Gombe, Adamawa, Taraba, Kano, Katsina da Kebbi da yammacin ranar.

“A yankin Arewa ta tsakiya, ana iya samun tsawa a sassan babban birnin tarayya, Kogi, Neja da Kwara da safe.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...