No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar NFF ta naɗa Éric Chelle a matsayin sabon kocin Super Eagles

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ta naɗa Éric Sékou Chelle a matsayin sabon kocin tawagar Super Eagles.

Naɗin na Chelle ya samu amincewa bayan taron da NFF ta gudanar a Abuja a ranar 2 ga watan Janairu, 2025, sannan aka kammala amincewa da shi a ranar 7 ga watan Janairu, 2025.

Chelle, wanda ke da shekaru 47, tsohon kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Mali, ya jagoranci kulab da dama kamar GS Consolat, FC Martigues, Boulogne, da MC Oran.

A lokacin da yake wasa, Chelle ya buga ƙwallo a kulab ɗin ƙasar Faransa irin su Martigues, Valenciennes, da Lens.

An haifi Chelle a ƙasar Côte d’Ivoire, daga mahaifi ɗan asalin Faransa da mahaifiya ‘yar ƙasar Mali.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar Manchester United ta sallami kocinta

Ya zaɓi yin wasa da Mali, inda ya taka leda a wasannin ƙasa guda biyar kafin ya yi ritaya daga wasannin ƙwallo.

Chelle ya jagoranci tawagar Mali daga 2022 zuwa 2024, inda ya kai su zuwa matakin kwata-fayinal a gasar Cin Kofin Afirka ta 2023 (AFCON).

Chelle ya karbi shugabancin Super Eagles bayan Finidi George ya murabus saboda rashin nasara a wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

Aikin Chelle na farko zai zama jagorantar Najeriya zuwa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...