Connect with us

Labarai

Hukumar NDLEA a Imo ta tabbatar da kashe jami’anta biyu tare da wasu jami’an tsaro uku

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeria (NDLEA) a ranar Laraba a Owerri ta tabbatar da kashe jami’anta biyu tare da wasu jami’an tsaro uku a ranar Talata a yankin ƙaramar hukumar Ehime-Mbano da ke Imo.

Kwamandan NDLEA a Imo, Abubakar Wali ya shaida wa manema labarai cewa an kashe kowane jami’in sojan saman Najeriya, ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaro da na farar hula a harin.

Ya ƙara da cewa kowane jami’in hukumar NDLEA da na sojojin ruwan Najeriya guda ɗaya ya samu raunuka sakamakon harbin da aka kai musu, kuma suna karɓar magani a asibitin koyarwa na jami’ar tarayya dake Owerri.

Wali ya ce ma’aikatan na rundunar ‘Forward Operation Base’ ne, rundunar tsaro da ta ƙunshi jami’an rundunar sojin Najeriya da kuma hukumar shige da fice ta Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NDLEA a Kaduna, ta tarwatsa haramtattun gidajen ƙwayoyi 13

Ya ce an ƙona motocin jami’an tsaron ne yayin da aka kwashe makamai da alburusai na jami’an da suka mutu, duk da cewa an ƙwato bindigar ta NDLEA.

“Abin takaici ne yadda muka rasa jami’ai biyu sannan muka samu ɗaya da rauni. “Ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a kama waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da gurfanar da su a gaban ƙuliya,” in ji Wali.

Shima da yake magana a kan wannan mumunan kisa, gwamnan Imo, Hope Uzodinma, ya bayyana takaicin yadda jami’an tsaro da ke taimaka wa wajen binciken laifukan da suka aikata a jihar ana kai hari.

Ya kuma buƙaci mazauna ƙauyukan da ke kewaye da su ba da kai bayanai masu amfani da za su kai ga cafke maharan da suka gudu zuwa ga hukumomin tsaro.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Mohammed Barde, wanda ya yi wa manema labarai jawabi a wurin da harin ya faru, ya ce maharan sun yi wa jami’an tsaro kwanton ɓauna ne a hanyar Obowo-Ehime Mbano.

Ya ƙara da cewa maharan sun yi harbin bindiga tare da harbin bama-bamai kan jami’an tsaro, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wasu daga cikinsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like