Connect with us

Labarai

Hukumar kula da birnin Abuja, ta gana da masana gine-gine

Published

on

Hukumar da ke kula da babban birnin tarayya Abuja ta hannun sashen kula da ci gaban ƙasa ta gana da ƙwararru a fannin gine-gine domin magance matsalar rugujewar gine-gine da filaye da aka yi watsi da su.

Daraktan sashen kula da ci gaban ƙasa, Mukhtar Galadima, ya bayyanawa manema labarai a Abuja, ranar Laraba, cewa hukumar ta damu da kawo ƙarshen abubuwan da ke haifar da gini marar inganci.

Ya ce: “A matsayinmu na ƙungiyar da ke da haƙƙi, dole ne mu himmatu wajen tunkarar al’amurran da suka shafi rugujewar gine-gine, dole ne mu yi aiki tare da ƙwararrun hukumomi masu kula da hukumomi.

“Muna musayar ra’ayi kan yadda za a daƙile barazanar rugujewar gine-gine a babban birnin tarayya.

KU KUMA KARANTA: Jami’an birnin Abuja sun ruguza kasuwar dare

“Taron zai taimaka mana wajen kafa kwamitin da zai ba da shawarwari kan yadda za a shawo kan matsalolin, ko da a baya amma a wannan karon za mu faɗaɗa shi.

“Za mu sanya shi ci gaba da kasancewa tare, tattaunawa da kulawa. Zai taimaka mana mu raba alhaki gami da ayyuka. ” Galadima ya bayyana cewa kwamitin da za a kafa nan ba da daɗewa ba zai kuma duba batutuwan da suka shafi gine-ginen da aka yi watsi da su da filaye da ba a gina su ba tare da samar da mafita.

Injiniya Cyril Nwafor, wanda ya wakilci Shugaban Majalisar Dokokin Injiniyoyi a Najeriya (COREN), ya buƙaci Majalisar Dokoki ta ƙasa ta aiwatar da shawarwarin da aka aika wa majalisar a shekarar 2010.

Ya jera shawarwarin don haɗawa da shigar ƙwararrun masu rajista kawai don gudanar da ayyukan da kuma ladabtar da waɗanda ke bayan ayyukan da suka gaza.

Sauran ƙwararrun hukumomin da suka halarci taron sun haɗa da Architect Registration Council of Nigeria (ARCON), Council of Registered Builders of Nigeria (CORBON) da dai sauransu.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Hukumar kula da birnin Abuja, ta gana da masana gine-gine - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like