No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) ta koka kan yawaitar tudun taƙaita gudu ‘bump’ ‘ba bisa ƙa’ida ba a babbar hanyar Gombe zuwa Yola.

Babban kwamandan hukumar FRSC a jihar Gombe Felix Theman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a jiya laraba.

A cewarsa, abin rage gudun ba kawai suna haifar da babban haɗari ga jama’a masu ababen hawa ba, har ma suna haifar da lalata hanyar da wuri wanda gwamnati ke kashe kuɗi wajen ginawa.

Ya ce tsakanin al’ummomin Cham da Bambam da ke kan babbar hanyar da ta ke da nisan kilomita 40, al’ummomi sun kafa ‘bump’ kusan tudu 57 ba gaira ba dalili, ya ƙara da cewa akwai kuma wasu 18 a kan hanyar Bambam zuwa garin Kaltungo. “

KU KUMA KARANTA: Jami’an hukumar FRSC za su fara kama motocin da lambarsu suka shuɗe

Direbobi sun ka sa bin ƙa’idojin gudu a wuraren da aka gina, al’ummomi kuma ba su bari hanyoyin su kasance ba yadda suke ba.

Yakamata al’umma su nisanta kansu daga wannan aikin ta taimakon kai domin yin hakan ba zai haifar da ɗa mai ido ba kawai amma a ƙarshe zai haifar da lalacewar hanyar da al’umma ke matuƙar buƙata.

“Ya kamata al’ummomi su yi ƙira ga mai kula da ayyuka na tarayya wanda alhakinsa shi ne kimanta matsalolin tsaro da nufin samar da mafita mafi aminci kamar yadda ya dace,” in ji kwamandan.

Ya kuma bayyana cewa aƙalla mutane bakwai ne suka mutu sannan 20 suka samu raunuka sakamakon haɗurra mota da aka yi a lokacin bikin ƙaramar Sallah da aka yi a jihar Gombe inda ya buƙaci masu ababen hawa da su riƙa tuƙa mota a ƙa’idance.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...