No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Hizba a Kano, ta haramta sauraron waƙar ‘Amanata’ ta Hamisu Breaker

Daga Shafaatu Dauda Kano

Rundunar Hisbah ta Jihar Kano ta nuna ɓacin ran ta, da bakin ciki akan wata waƙa da mawaƙi Hamisu Breaker, ya rera mai suna Amana ta, inda rundunar tace akwai kalaman batsa a cikin ta.

Mataimakiyar babban kwamandan rundunar a bangaren Mata Dr. Khadija Sagir, ce tayi ala wadai da wakar, sannan ta nemi matasa su dena sauraron wakar.

KU KUMA KARANTA:Hisbah a Kano ta rushe wurin da ake cewa sawun Annabi (SAW) ne ya fito

Hisbah tace wakar na dauke da abubuwan da ke goyon bayan aikata alfasha, musamman yadda mata ke rawa da kuma amfani da kalmomin batsa a cikin bidiyon wakar.

Dr. Khadija ta kara da cewa bisa abinda ke cikin wakar, an dauke ta a matsayin haramun a karkashin koyarwar addinin Musulunci.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...