No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Hisbah a Kano, ta kama mutane 62 da ake zargi da baɗala a Dawakin Kudu

Daga Jameel Lawan Yakasai

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce ta kama maza 27 da ƴan mata 35 da ake zargi da aikata badala a makarantar NITT da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a Kano.

Hisbah ta bayyana cewa, jami’anta sun kai samame wurin a ranar Lahadin nan bayan samun bayanan sirri da ƙorafe-ƙorafe.

KU KUMA KARANTA: Hukumar Hisbah a Yobe ta kama kwalaben giya, ta rufe gidajen Karuwai a Gashuwa

Jamiʼan Hisbar sun ce, sun tarar da waɗanda ake zargin suna gudanar da taro da ake alakantawa da ayyukan badala.

Tuni aka taho da su ofishin hukumar domin ci gaba da bincike, kafin ɗaukar mataki na gaba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...