Connect with us

DSS

Hukumar DSS ta ƙwato makamai a jihohi daban-daban biyo bayan hare-haren siyasa a Kano

Published

on

Ƙasa da sa’o’i saba’in da biyu a fara zaɓen 2023, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta bankado maɓoyar masu miyagun laifuka tare da ƙwato muggan makamai a wurare daban-daban a faɗin ƙasar nan ciki har da wata kadara da ke kan titin filin jirgin sama a karamar hukumar Nasarawa na jihar Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ta DSS, Dakta Peter Afunanya, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis inda ya musanta zargin da ake na cewa ayyukan hukumar a jihar Kano na kai hari kan wata jam’iyyar siyasa.

Kayayyakin da aka ƙwato daga kadarorin a jihar Kano sun haɗa da bindiga, wuƙaƙe, takubba, da ƙananan wuƙaƙe na jack da dai sauransu.

Hakazalika, hukumar ta DSS ta kama wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihohin Kaduna da Zamfara, ciki har da wani mai suna Aliyu Yahaya da ke harƙallar bindigu ga wani da ake zargin ‘yan fashi da makami mai suna Kachalla Damina da ke aiki a kewayen Dansadau a jihar Zamfara.

KU KUMA KARANTA: Yadda jami’an DSS suka harbe matashi a taron siyasa a Gombe

Makaman da aka ƙwato sun haɗa da bindigogin RPMG da caches na alburusai.

Hukumar ta kuma kama wani Fajuwon Isaac a jihar Delta tare da kwato harsasan bindiga sama da dubu huɗu da ɗari biyar da sauran makamai, yayin da a jihar Anambra aka kama wasu mutane huɗu ɗauke da bindigar AK-47 ɗaya, da kuma harsasan bindiga kusan dubu huɗu na Ake 47 alburusai.

Yayin da take ba da tabbacin tsaro ga ɗaukacin ‘yan Najeriya kafin zabe da lokacin zaɓe da kuma bayan zaɓe, hukumar ta DSS ta yi ƙira ga masu zaɓe da su kiyaye doka da oda.

“Hukumar DSS ta tabbatar da aniyar ta na gudanar da atisayen cikin lumana, sannan ta yi alƙawarin kasancewa tsaka-tsaki, ƙwararru, da kyakkyawar ɗabi’ar ma’aikatanta ga tsarin dimokuradiyya, “in ji Afunanya.

“Za ta ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na yaɗa aiki kan lokaci, aiki, da kuma bayanan sirri da suka wajaba don dabara, aiki, da yanke shawara ko da bayan zaɓen.”

A wani labarin kuma wasu ‘yan daba da ‘yan bangar siyasa sun kai hari kan magoya bayan jam’iyyar NNPP a Kano inda suka kashe mutum 1 tare da lalata motoci da dama na Kwankwaso na NNPP.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Hukuma tayi ram da Alasan Ado Doguwa, bisa tuhumar kisan kai | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Yadda aka kama wata mata ɗauke da kayan zaɓe na INEC a Legas | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Yadda aka kama wata mata ɗauke da kayan zaɓe na INEC a Legas - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

DSS

DSS ta sako wacce ta soki gwamnatin Kaduna a Facebook

Published

on

An sako Aisha Galadima, wacce take kare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da jami’an tsaron farin kaya (DSS) suka kama don yin bincike.

Aminiya ta ruwaito yadda aka damƙe ’yar Jam’iyyar APC  a Kaduna bisa wani rubutu da ta yi a Facebook kan Gwamna Uba Sani.

A cewar majiyoyi, Aisha Galadima ta soki kalaman Gwamna Uba Sani na ƙarshe a kan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai.

Wata ƙwabciyarta ta ce, an kama ta ne a unguwar Tudun Wada a Kaduna a ranar Lahadi da yamma, kuma wata abokiyarta ta bayyana cewa wayar Aisha a kashe take bayan tsare ta da aka yi.

Sai dai babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Muhammad Lawal Shehu, ya ce ba shi da masaniyar kama ta.

“Ban san an kama wata mata da ta rubuta munanan kalamai a kan Gwamna ba. Amma kuna iya mika tambayoyinku ga hukumar DSS ba gwamnatin jihar Kaduna ba,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: El-Rufai ya bar wa jihar Kaduna ɗimbim bashi – Gwamnan Uba Sani

An sake ta ne bayan da ta kai kusan awa 24 a hannun hukuma.

Da aka tuntuɓi Aisha, ta tabbatar da sakin nata, inda ta ce jami’an hukumar sun tursasa tare da dukan ta.

“Ina cikin ɗakina zan yi wanka sai suka shigo suka ja ni. Na ga motar su ƙirar Hilux hudu a wajen gidan. Suka tura ni ciki suka wuce,” in ji ta.

A cewarta, (DSS) sun zarge ta da yin wani rubutu a kan gwamnan a watan Fabrairu.

Continue Reading

DSS

DSS sun cafke shugaban ƙungiyar Miyatti Allah

Published

on

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo, kan kafa rundunar sa-kai ta Fulani a jihar Nasarawa.

Wasu shugabannin ƙungiyarsa ta Kautal Hore kuma makusanta sun tabbatar da batun kama Bodejo a jiya Talata.

Sun ce jami’an DSS tare da wasu sojojin Najeriya suka kama shi a garin Lafiya babban birnin jihar Nasarawa.

Sai dai sun ce suna bin bahasi domin ba su san inda aka tafi da shi ba.

A ranar Laraba 17 ga watan Janairu Bello Badejo ya ƙaddamar da rundunar a garin Lafiya inda ya ce za ta taimaka wajen yaƙar ɓarayi da ɓata-gari daga cikin Fulani.

KU KUMA KARANTA: An ɗaure Sarkin Fulani da ‘yan uwansa 2 kan garkuwa da mutane

Bayanai na cewa jami’an tsaron Najeriya sun kama Bodejo ne kan fargabar cewa ƙirƙiro da ƙungiyar sa-kai zai iya janyo tashin hankali a faɗin ƙasar, kuma kasancewar ba ta da rijista da hukumar farin kaya ta DSS.

Continue Reading

DSS

DSS ta ce shugabanta bai sace kuɗin tallafi na ma’aikatan hukumar ba

Published

on

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya a Najeriya DSS ta musanta zarge-zargen da ake yi kan cewa babban daraktan hukumar Magaji Yusuf Bichi ya yi sama da faɗi da kuɗin tallafi na ma’aikatan hukumar.

Mai magana da yawun hukumar Peter Afunanya ne ya fitar da sanarwar inda ya musanta zargin da wani Jackson Ude ya yi a shafin X wanda ya yi zargin shugaban DSS din da kwashe kuɗin.

Afunanya ya tabbatar da cewa babu wasu kuɗi da aka bai wa hukumar a halin yanzu domin ma’aikata kuma da zarar an fitar da waɗannan kuɗaɗe za a bai wa ma’aikatan hakkinsu.

“Hukumar tana son sanar da cewa zarge-zargen da ake yi ba gaskiya bane. Hukumar na son tabbatar da cewa daraktan hukumar ko wani mai aiki da umarnin shi, babu a cikinsu wanda ya sace kuɗin tallafin da aka bai wa ma’aikata.

KU KUMA KARANTA: Sojoji da DSS sun daƙile yunkurin Boko Haram na kai hari a Kano

“Babu wani tallafi da aka bai wa hukumar kuma da zarar an bayar da shi, za a bai wa ma’aikatan hakkinsu,” in ji sanarwar.

Hukumar ta DSS ta buƙaci jama’a su yi watsi da ƙarerayin da ake yaɗawa waɗanda ke kawo rabuwar kai da kuma rikici.

Haka kuma hukumar ta tabbatar da cewa daraktan na DSS zai ɗauki matakai na shari’a dangane da lamarin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like