No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya ta DSS, ta kama Fiddausi Musa Ahmadu, mai shekaru 23, bayan ta yi barazanar kashe kanta tare da kashe duk waɗanda ke da alhakin nasarar jam’iyyar ‘All Progressives Congress’ (APC), ɗan takarar gwamna a Kano, Nasiru Yusuf Gawuna.

Jaridar Alfijir ta rawaito  wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta tabbatar da kama Fiddausi Musa Ahmadu.

KU KUMA KARANTA: Hukumar DSS a Nasarawa, ta kama jami’an NASEMA bisa zargin karkatar da kayan abinci

A cikin faifayin bidiyo, an ji Fiddausi tana cewa za ta kai wa babban alƙalin kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamna hari, inda ta yi gargaɗin cewa duk inda ta gan ta, ba za ta damu da riƙe ta da bom.

Hakazalika, Fiddausi wanda ke sanye da jar hula, ta gargaɗi Nasiru Yusuf Gawuna ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC da cewa, “ka da ka kuskura ka bayyana inda kake, in ba haka ba, ba na damu da buga maka rigar bama-bamai .

Haka kuma na kai wa mataimakin shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima hari, inda ta ɗora masa laifin dambarwar jam’iyyar NNPP a Kano.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...