Connect with us

Labarai

Hukumar ba da agajin gaggawa ta tarayya ta yi gargaɗin samun iska mai ƙarfi a jihohi 12

Published

on

Daga Haruna Yusuf

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta tarayya ta yi gargaɗin cewa jihohin da ke kewaye da babban birnin tarayya za su fuskanci iska mai ƙarfi nan da kwanaki uku masu zuwa.

A cikin wata sanarwa da shugaban hukumar ta FEMA, Nkechi Isa, ya sanyawa hannu a ranar Laraba, hukumar ta ce tana yin wannan gargaɗin ne biyo bayan hasashen yanayi mai tasiri da hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta yi.

“Jihohin da ke daura da babban birnin tarayya, kamar Nasarawa, Neja da Kaduna za su fuskanci iska mai ƙarfi nan da kwanaki uku masu zuwa.

Jihohin Kebbi, Sokkwato, Zamfara, Katsina, Bauchi, Yobe, Gombe, Borno da Adamawa su ma za su fuskanci iska mai ƙarfi.

Hasashen ya yi gargaɗin cewa matsakaicin haɗari na iya faruwa saboda iska mai ƙarfi, ”in ji sanarwar.

Ya bayyana cewa mai yuwuwar iskar mai ƙarfi ta iya haifar da ɓarkewar mutane da kuma keɓantacce na lalacewar gine-gine masu rauni.

KU KUMA KARANTA: Guguwa mai ƙarfi ta kashe mutane 11 a Pakistan

Ya ƙara da cewa, “Tun da cewa sauyin yanayi a wasu jihohin nan, musamman Nasarawa, na iya yin tasiri a babban birnin tarayya, FEMA na sa ido sosai kan lamarin.”

A halin da ake ciki, Darakta Janar na FEMA, Dakta Abbas Idriss, ya ce an sanya ƙungiyoyin bincike da ceto na hukumar cikin shirin ko-ta-kwana, ya kuma gargaɗi mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan a lokacin da ake ruwan sama mai ƙarfi da kuma guje wa tuƙi a cikin tafkin ruwa.

Ya kuma yi ƙira ga mazauna yankin da su share magudanan ruwa da suka toshe, sannan su guji yin gini a magudanan ruwa, tare da ba su tabbacin cewa hukumar ta himmatu wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, ya kuma buƙaci a yi amfani da lamba 112 na kyauta idan har aka samu matsala gaggawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like