No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar ƙidaya ta ƙasa, (NPC), ta ce an ɗage ƙidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023 ne saboda shirin miƙa mulki na gwamnati da kuma yanayin da ƙasar ke ciki bayan zaɓe.

Inuwa Jalingo, manajan ƙidaya na shekarar 2023 kuma darakta, hukumar ƙidaya ta ƙasa NPC, ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Abuja ranar Lahadi.

Jalingo wanda ya tabbatar da shirin hukumar na ƙidayar jama’a a shekarar 2023, ya ce NPC ta shirya yin ƙidayar jama’a na farko a Najeriya.

Ya ce hukumar ta samu nasara mafi girma a dukkan fannoni ta fuskar shirye-shiryen.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Tarayya ta ƙara ɗage ƙidayar jama’a

“Mun cimma daidaiton ƙasashen duniya don ƙidayar cikin tsari. “Kimanin na’urori na na zamani guda 450,000 an sayo kuma an rarraba su ga dukkan ƙananan hukumomi,” in ji shi.

Mista Jalingo ya ce duk da haka, gwamnati na ci gaba da aiki, yana mai fatan gwamnatin mai jiran gado za ta ci gaba da samun nasarorin da aka samu domin gudanar da ƙidayar.

Manajan ƙidayar ya yabawa gwamnatin Buhari bisa goyon bayan da ta bayar, inda ya ce hukumar ta samu nasarar horar da malamai kusan 60,000 a faɗin kasar nan.

“Duk wanda ya ce ba mu shirya ba dole ne ya faɗi haka cikin jahilci,” in ji shi. Mista Jalingo ya nanata fa’idar ƙidayar jama’a da ba ta rasa nasaba da tsare-tsare na tattalin arziƙin ƙasa da samar da bayanan tsare-tsare na gudanarwa.

Ya ce hukumar ta iya tattara ‘yan Najeriya domin a yi ƙidayar da duk wani bayani da ake buƙata domin a samu nasarar ƙidayar jama’a.

Hukumar NPC ta ɗage ƙidayar yawan jama’a da gidaje da aka shirya tun daga ranar 3 ga Mayu zuwa 7 ga Mayu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...