No menu items!

Sample Page Title

Date:

Falasɗinawa a faɗin Gabar Yammacin Kogin Jordan sun yi ta sowa da daga tutocin Falasɗinu da na Hamas da kuma maratayin kaffiyeh bayan Isra’ila ta saki Falasɗinawa 39 da take tsare da su shekara da shekaru.

“Ina cike da farin cikin amma ‘yancina ya samu ne bayan mutane da dama sun yi shahada,” in ji Marah Bakir, mai shekara 24, inda take magana a kan kusan mutum 15,000 da Isra’ila ta kashe a Gaza tun lokacin da ta ƙaddamar da hare-hare.

Hanan al Barghouti, mai shekara 58, wadda aka saka daga kurkukun Isra’ila bayan ta kwashe wata biyu, ta jinjina wa Hamas da shugabanninta da al’ummar Gaza.

Ta yi addu’ar “Allah ya saka musu da alheri. Idan ba domin al’ummar Gaza suke aiki ba da ba za mu samu ‘yanci ba. “Muna cikin kurkuku muna shan ukuba. Matsiyata ne. Sun ci zarafinmu, sun wulakanta mu. Amma hakan bai sa mun sarayar da mutuncinmu ba, kuma muna godiya bisa wannan jajircewa da aka yi.”

Ga hotunan wasu daga cikin mata da matasa da aka saka daga gidajen yarin Isra’ila.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...