Connect with us

Ƙasashen Waje

Hezbollah ta ce ta halaka sojojin Isra’ila da dama a wani hari kan sansaninsu

Published

on

Ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon a ranar Asabar ta ce ta kai hari kan sansanin sojin Isra’ila na Birket Rishe da ke kan iyakar ƙasar Lebanon da Isra’ila inda ta ce ta halaka sojojin da dama da raunata wasu.

Ƙungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar inda ta ce ta yi amfani da makamai mai linzami wurin kai harin.

Rikici tsakanin Hezbollah da kuma sojojin Isra’ila ya ƙara ƙazanta tun bayan da yaki ya rincaɓe tsakanin sojojin Isra’ila da dakarun Hamas a ranar 7 ga watan Oktoba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta kama mutum 15 a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan

Published

on

Isra'ila ta kama mutum 15 a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan

Isra’ila ta kama mutum 15 a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan

Aƙalla Falasɗinawa 15 Isra’ila ta ƙara kama a wani samame da ta kai a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da ta mamaye, kamar yadda wata ƙungiya da ke kula da fursunoni ta tabbatar a ranar Lahadi.

Sojojin sun kai samamen ne a Hebron da Tubas da Ramallah da Birnin Kudus, kamar yadda hukumar da ke kula da waɗandake tsare da kuma ƙungiyar kula da fursunoni Falasɗinawa suka bayyana a wata sanarwa ta haɗin gwiwa.

KU KUMA KARANTA: Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

“Waɗanda aka kama na fuskantar cin zarafi da duka, da kuma barazana ga iyalansu, baya ga yawaitar ayyukan zagon kasa da lalata gidajen ‘yan ƙasar,” kamar yadda sanarwar ta ƙara da cewa.

Kamen na ranar Lahadi ya kawo adadin Falasɗinawa da Isra’ila ta kama tun daga 7 ga watan Oktoba a Yammacin Kogin Jordan zuwa 9,550 a cewar alkaluman Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Published

on

Dakta Mas'ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Waye Dakta Mas’ud Pezeshkian sabon shugaban ƙasar Iran na 9 cikin shekaru 45 ataƙaice?

An haife shi a ranar 29 ga Satumba, 1954, a Mahabad, a yammacin lardin Azarbaijan, Dakta Mas’ud Pezeshkian ya wakilci birnin Tabriz da ke arewa maso yammacin kasar a majalisar dokokin Iran ta 12.

Ya riƙe muhimmin muƙamai a majalisar a Hukumomi daban-daban matakin gwamnatin tarayya, kuma ya zama ministan lafiya a lokacin mulkin Shugaba Mohammad Khatami (2001-2005). Duk da cewa an tsige shi bayan wasu lokuta saboda gaza cimma wasu ayyuka da kawo sauyi.

An zaɓe Pezeshkian a majalissar 8th, 9th, 10th, and 11th. A tsakanin shekarar 2016 zuwa 2020, ya kuma rike mukamin mataimakin shugaban majalisar na farko. A baya dai ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2013 da 2021 amma ya kasa samun nasara a lokuta biyun.

KU KUMA KARANTA: An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Dr. Mas’ud Pezeshkian likitan zuciya ne kuma me koyarwa, ya yi aiki a matsayin shugabar Jami’ar Tabriz ta Kimiyyar kiwon lafiya, kuma a halin yanzu memba ne na ma’aikatan ilimi a wannan babbar jami’a a arewacin Iran.

Bayan da ya samu amincewa daga babbar hukumar da ke sa ido kan zabukan kasar na ya tsaya takara a zaben na ranar 28 ga watan Yuni a watan da ya gabata. Ya gabatar da tsare-tsarensa, inda ya jaddada muhimmancin damka ayyuka ga kwararru kuma masu ilimi a gwamnatinsa.

Haka nan kuma ya bayyana Javad Zarif, tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran a matsayin zabinsa na shugabancin ma’aikatar harkokin wajen kasar, yayin da ya sha alwashin aiwatar da umarnin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Pezeshkian a hukumance ya shiga takarar neman kujerar shugaban kasar a ranar 1 ga watan Yuni, rana ta uku ta rajista, a ma’aikatar harkokin cikin gida da ke Tehran, tare da rakiyar gungun magoya bayanta.

A muhawarar zagaye na biyu na zaben shugaban kasa, Pezeshkian ya bayyana mahimmancin kiyayewa da cika alkawura a matsayin wani muhimmin al’amari na kiyaye kyawawan halaye.

Ya jaddada muhimmancin nuna girmamawa ga daidaikun mutane, tabbatar da jin muryoyinsu, da bayar da shawarwari kan ayyuka bisa ka’idojin adalci da adalci.

Tsohon ministan lafiya ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da amana ke takawa wajen ciyar da al’umma gaba, tare da jaddada cewa gaskiya na da matukar muhimmanci wajen samar da amana a tsakanin al’umma.

Pezeshkian ya jaddada muhimmancin ba da fifiko kan dangantaka da kasashen dake makwabtaka da ita, da fadada huldar dake tsakanin kasashen duniya don bunkasa ci gaban kasar.

A lokuta da dama, ya nanata kudurinsa na mutunta tsarin dokokin Jamhuriyar Musulunci da kuma manufofin da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamene ya bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Published

on

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra'ila

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar Hezbollah mai da ke Lebanon ta ƙaddamar da hare-haren rokoki fiye da 200 da jirage marasa matuƙa zuwa arewacin Isra’ila, a wani martani na kisan ɗaya daga cikin manyan kwamandojinta.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe sojanta da dama a hare-haren, na Hezbollah.

Sojojin na Isra’ila sun kuma ce sun mayar da martani kan mayaƙan ƙungiyar da sansanoninta da ke kudancin Lebanon.

Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ce mutum guda ya mutu a wani harin jirgi maras matuƙi da Isra’ila ta kai garin Houla.

Hare-haren na baya-bayan nan, sun kasance mafiya muni cikin watanni tara tsakanin kan iyakokin ƙasashen biyu.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

An kashe ɗaya daga cikin kwamandojin Hezbollaha wani hari ta sama da Isra’ila ta kai birnin Tyre na ƙasar Lebanon.

Mohammed Nimah Nasser, ya kasance ɗaya daga cikin manyan jagororin ƙungiyar, kafin kisan nasa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like