No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata tirela da ke ɗauke da kusan mutum 230 a cikinta ta yi hatsari a Jihar Neja, inda aƙalla mutum 25 suka rasu nan take.

Bayanai sun nuna motar ta yi hatsarin ne ita kaɗai a ƙauyen Takalafiya da ke kan babbar hanyar Yawuri a ƙaramar Hukumar Magama ta Jihar Neja.

A cewar Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan Jihar, Bologi Ibrahim, Gwamnan Jihar, Mohammed Umar Bago, ya damu matuka da hatsarin sannan ya buƙaci direbobi su daina karya dokokin tuƙi.

Ya ce hatsarin, wanda aka yi ranar Talata ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a, wanda ya sa motar ta ƙwace daga hannun direbanta.

Bayanai sun nuna tirelar dai ta taso ne daga Jihar Sakkwato ɗauke da mutum 229, waɗanda suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara a cikinta.

KU KUMA KARANTA: Mutum 4 sun mutu a Abiya, wasu sun jikkata a hatsarin mota

Rahotanni sun ce nan take mutum 25 suka mutu, yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka kuma yanzu aka garzaya da su Babban Asibitin Kontagora, inda suke samun kulawa.

Kazalika, waɗanda suka rasu yanzu haka an kai gawarwakinsu ɗakin adana gawarwaki na asibitin na Kontagora.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...