Hatsarin tirela a Ibadan ya murƙushe mutane 25

0
36
Hatsarin tirela a Ibadan ya murƙushe mutane 25

Hatsarin tirela a Ibadan ya murƙushe mutane 25

Wani hatsarin mota ya laƙume rayukan ’yan arewa 18 da wasu mutane 7, a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Hatsarin da ya laƙume rayuka 25 a ranar Talata, ya auku ne a daidai mararrabar Agbowo Ajao a kan babbar hanyar Oyo zuwa Iwo.

Wani da lamarin ya auku a kan idanunsa ya ce burki ne ya ƙwace daga direban wata tirela da ke ɗauke da banduran kwanukan rufi inda a nan take ya danne wasu ƙananan motoci uku masu ɗauke da fasinjoji a cikinsu.

Sarkin Hausawan Ojo Tudun-Sunnah da lamarin ya auku a kusa da fadarsa, ya shaida wa Aminiya cewa “a binciken da muka gudanar mun gano cewa ɗaya daga cikin motocin da haɗarin ya rutsa da su wata motar bas ce mai ɗaukar mutane 18 da ta taso daga Jihar Jigawa a kan hanyar zuwa Legas.”

KU KUMA KARANTA: Hatsarin jirgin ruwa ya laƙume rayukan mutane 9 a Zamfara

Sarkin Hausawan ya ce duka fasinjoji 18 da ke cikin wannan motar bas sun gamu da ajalinsu.

Ya ce, “yanzu haka al’ummar Hausawa a nan Ojo Tudun-Sunnah sun taimaka da kudin sayen likkafani domin suturta waɗannan ’yan uwa Musulmi da za a yi masu jana’iza da binne su a makabartar Akinyele inda aka saba binne musulmi ’yan Arewa da suka riga mu gidan gaskiya.”

Sauran mutanen da ke cikin ƙananan motocin da tirelar ta murƙushe an kwashe gawarsu zuwa Asibiti.

Har zuwa lokacin rubuta wannan rahoto babu wani bayani a hukumance da aka samu dangane da wannan hatsari.

Sai dai binciken ya nuna cewa kafin isowar jami’an tsaro an ga jama’a suna kai ɗauki domin ceton waɗanda suka samu raunuka a wajen hatsarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here