No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla mutane shida ne suka rasa rayukansu yayin da ɗaya ya jikkata a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a Akure, babban birnin jihar Ondo a yammacin ranar Talata.

Hatsarin wanda ya auku a kan titin Akure-Owo, ya rutsa da wata mota ƙirar man diesel ja ɗaya da Toyota Sienna mai launin toka mai lamba FFN 310 PU.

Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 1:39 na rana a kimanin kilomita 3 daga filin jirgin saman Akure. Da yake tabbatar da faruwar hatsarin a wata sanarwa da ya rabawa LEADERSHIP, kwamandan hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Ondo, Mista Ezekiel SonAllah, ya ce manya maza shida ne suka mutu yayin da wata babbar mace ta samu rauni a cikin mutane bakwai da lamarin ya rutsa da su.

KU KUMA KARANTA: Mutum biyu sun mutu, biyar sun jikkata a hatsarin mota a Ondo

SonAllah ya dangana musabbabin faruwar hatsarin da cin zarafi (SPV), wuce gona da iri (WOV), da kuma rashin kulawa (LOC).

Kwamandan FRSC ya bayyana cewa kayayyakin da aka ƙwato daga wurin da hatsarin ya auku sun haɗa da kuɗi da wayoyi.

A cewarsa, an miƙa kayayyakin ne ga jami’an ‘yan sanda daga Ogbese da ke ƙaramar hukumar Akure ta Arewa.

Ya kuma bayyana cewa an ajiye gawarwakin shidan a babban ɗakin ajiyar gawa na babban asibitin Akure, yayin da aka kawar da cikas daga hanyar domin zirga-zirga kyauta.

Don haka Son Allah, ya yi ƙira ga masu ababen hawa da su riƙa bin ƙa’idojin tuƙi da aka ƙayyade, kuma dole ne direbobin ‘yan kasuwa su tabbatar sun sanya na’urorin da ke hana saurin gudu a motocinsu.

“Ya kamata direbobinmu su kasance masu lura da tsaro a kowane lokaci kuma ka da su wuce idan babu lafiya.

“Ba wai kawai ya kamata fasinjoji su gargaɗi direbobi idan sun wuce gona da iri amma kuma su kai rahoto ga jami’an tsaro da ke kula da manyan hanyoyin,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...