No menu items!

Sample Page Title

Date:

Harin da Isra’ila ta kai a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama

Aƙalla Falasɗinawa 15 da suka haɗa da ƙananan yara ne suka mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata, a wani harin da Isra’ila ta kai kan wani matsuguni da ke Khan Younis a kudancin Gaza a yammacin Lahadi, a cewar wata majiyar kiwon lafiya.

Shaidu sun ba da rahoton cewa, an kai harin ne a makarantar Ahmed Abdel Aziz, inda ɗaruruwan fararen hula da suka rasa matsugunansu suka nemi mafaƙa.

KU KUMA KARANTA: Farmaƙin Isaraila ta sama ya kashe aƙalla mutane 18 a Gaza.

Hukumar tsaron kiyaye farar hula ta Gaza ta tabbatar da harin, inda ta ce tawagogin likitocin sun gano gawarwaki da dama. Sai dai har yanzu ba a fayyace adadin yaran da abin ya shafa ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...