No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mutane da dama ne suka mutu yayin da wasu suka jikkata sakamakon wani harin bam da Isra’ila ta kai a unguwar Shujaiya da ke birnin Gaza a cewar kafar yaɗa labaran Falasɗinu.

Kamfanin dillancin labaran Falasɗinu Wafa, ya bayar da rahoton cewa, an ci gaba da kai hare-haren bama-bamai a wasu yankuna da dama a Gaza.

Hukumar ta ce, Isra’ila ta fi kai hare-haren a yankunan gabashin Khan Younis da kuma gabar tekun Rafah da ke kudancin Gaza, yayin da jiragen yakin Isra’ila suka fi kai hari a tsakiyar Gaza.

A ranar 1 ga watan Disamba ne Isra’ila ta sake kai farmakin soji a Zirin Gaza bayan kawo ƙarshen tsagaita wuta na tsawon mako guda da kungiyar Hamas ta Falasɗinu.

Aƙalla Falasɗinawa 17,177 aka kashe yayin da wasu fiye da 46,000 suka jikkata sakamakon hare-haren wuce gona da iri da aka kai a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba bayan harin ba-zata da ƙungiyar Hamas ta kai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...