No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce har yanzu a hukumance ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar ba su sanar da ita matakinsu na fita daga cikinta ba.

A ranar Lahadi da hantsi ƙasashen uku suka fitar da sanarwa cewa sun fice daga ƙungiyar saboda ta gaza taimaka musu wurin shawo kan rashin tsaron da ke addabasu da ma sauran ƙalubalen da suke fama da su.

“Har yanzu Hukumar ECOWAS ba ta samu bayani a hukumance daga ƙasashen uku ba da ke nuna cewa sun fita daga cikinta,” a cewar wata sanarwa da ECOWAS ta wallafa a shafinta na X.

Kungiyar ta ce ta yi mamakin “wannan mataki.”

ECOWAS ta ƙara da cewa tana “aiki babu kakkautawa da waɗannan ƙasashe domin ganin an dawo da tsarin mulki.”

KU KUMA KARANTA: Jamhuriyar Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga ECOWAS

“Burkina Faso, Nijar, da Mali mambobinmu ne masu matuƙar muhimmanci kuma hukumar nan za ta yi baƙin ƙoƙarinta wurin samar da mafita ga rikicin siyasar da suke ciki.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...