Connect with us

Labarai

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Published

on

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi - Hajiya Aisha Ibrahim

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Wata mata mai gidan abinci ta faɗa tarkon ’yan damfara inda aka ba ta kwangilar bogi ta samar da abinci na kwanaki uku kan kuɗi Naira miliyan 13.

An ba Hajiya A’isha Ibrahim kwangilar bogin ce da sunan za ta ciyar da mabuƙata dubu tara a ƙananan hukumomi uku na jihar.

Labarin Hajiya Aisha da ke sana’ar abinci a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ya karaɗe gari ne bayan ta yi bidiyon halin da take ciki a kafofin sada zumunta.

Hakan ya sa gwamnan jihar, Sanata Bala Abdulqadir Muhammad ya shiga tsakani ya biya ta kuɗin data kashe wajen yin abincin, aka karɓi abincin aka raba wa masu buƙata.

A zantawar datayi da manema labarai, Hajiya Aisha ta ce wani mutum ne ya tuntuɓe ta da ya ba ta kwangilar samar da abinci ga mutane 9,600 a ƙananan hukumomin Bauchi, Alkaleri, da Kirfi.

A yayin da take bayyana irin halin da ta shiga, duk da cewa ba ta bayyana sunan mutumin da ya ba ta kwangilar bogin ba, Hajiya Aishah ta ce mutumin ya ba ta tabbacin cewa nan ba da daɗewa ba za a rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangilar, kuma ba za a saka ta cikin hadari ba.

“Ya dage cewa in ci gaba da kwangilar saboda ba a sanya hannu kan yarjejeniyar ba, amma za a ba ni takardan yarjejeniyar yin kwangilar lokacin da aka sanya hannu,” inji Aisha.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya za ta fara farautar ma’aikatan da suke da shaidar karatun bogi

Ta ce ta amince da tabbacin da ya ba ta saboda ta san yadda kungiyoyi masu zaman kansu suke yi, in suka bada irin wannan aiki, kuma suna biya bayan an kammala aikin.

Daga nan sai ta saki zuciyarta ta ci gaba da bin umurnin mutumin ta samo ma’aikata ta suka kwana suna aikin yin abinci.

Ta ce da suka kammala sai ta ƙira mutumin da nufin ta san waɗanda za su karɓi abincin, sai ya ce ta jira yana jiran a ba shi umurni tukuna.

“Bayan karfe 1 na rana ban ji ɗuriyarsa ba, sai na tafi ofishinsa, ya ce in jira yana jiran umarni.
“Bayan uku na yamma na fara ƙiran sa sau da yawa, amma ba ya ɗauka.

“Da muka je ofishinsa da mijina da misalin karfe biyar na yamma, sai aka ce mana ba ya nan.
“Tun daga lokacin ya ƙi ɗaukar wayata har ƙarfe biyar na yammaci.”

Hajiya A’isha ta ce ta yi matukar kaɗuwa da lamarin domin ta karɓi basussuka ne ta yi abincin.

Da ta kasa samun mutumin, sai ta shiga kafafen sada zumunta tana neman taimako.

Ta ce “Kwamishiniyar jin ƙai da bada agaji na Jihar Bauchj Hajiya Hajara Yakubu Wanka ta ƙira ni inda ta ce Gwamna ya ga bidiyona a intanet kuma ya umarce ta da ta biya ni diyya.

“Ina godiya ga Gwamna Bala Mohammed kan matakin da ya ɗauka na ceto ni cikin gaggawa.”
Hajiya Aisha ta ce gwamnati ta biya kuɗin da ta sayi kayan Naira miliyan 7.5 ba, kuma ta karɓi abincin aka rarraba shi wa masu bukata.

Da yake mayar da martani kan lamarin, babban sakatare a ma’aikatar, Alhaji Shuaibu Alhaji Muhammad, ya bayyana cewa asalin kuɗin kwangilar naira miliyan 13 ne, amma gwamnatin jihar ta biya diyya na ainihin kuɗin kayan abinci da Hajiya Aisha ta saya.

Wani abu daya ja hankalin jama’a shi ne Hajiya Aisha ta zabi kada ta bayyana sunan mutumin da ya yaudare ta, duk da cewa ta yi wa jami’an tsaro cikakken bayani.

Ta kuma gargaɗi jama’a game da masu zamba a asusun banki da za su ce za su rika neman tallafi da sunanta.

Kalli bidiyo a nan:

Labarai

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Published

on

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

 

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).

“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.

Continue Reading

Labarai

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Published

on

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

 

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.

Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.

Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.

Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:

* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.

* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.

* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.

* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.

* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.

* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.

Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.

Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.

Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.

KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano

Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.

An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.

Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like