Connect with us

Labarai

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Published

on

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi - Hajiya Aisha Ibrahim

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Wata mata mai gidan abinci ta faɗa tarkon ’yan damfara inda aka ba ta kwangilar bogi ta samar da abinci na kwanaki uku kan kuɗi Naira miliyan 13.

An ba Hajiya A’isha Ibrahim kwangilar bogin ce da sunan za ta ciyar da mabuƙata dubu tara a ƙananan hukumomi uku na jihar.

Labarin Hajiya Aisha da ke sana’ar abinci a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ya karaɗe gari ne bayan ta yi bidiyon halin da take ciki a kafofin sada zumunta.

Hakan ya sa gwamnan jihar, Sanata Bala Abdulqadir Muhammad ya shiga tsakani ya biya ta kuɗin data kashe wajen yin abincin, aka karɓi abincin aka raba wa masu buƙata.

A zantawar datayi da manema labarai, Hajiya Aisha ta ce wani mutum ne ya tuntuɓe ta da ya ba ta kwangilar samar da abinci ga mutane 9,600 a ƙananan hukumomin Bauchi, Alkaleri, da Kirfi.

A yayin da take bayyana irin halin da ta shiga, duk da cewa ba ta bayyana sunan mutumin da ya ba ta kwangilar bogin ba, Hajiya Aishah ta ce mutumin ya ba ta tabbacin cewa nan ba da daɗewa ba za a rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangilar, kuma ba za a saka ta cikin hadari ba.

“Ya dage cewa in ci gaba da kwangilar saboda ba a sanya hannu kan yarjejeniyar ba, amma za a ba ni takardan yarjejeniyar yin kwangilar lokacin da aka sanya hannu,” inji Aisha.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya za ta fara farautar ma’aikatan da suke da shaidar karatun bogi

Ta ce ta amince da tabbacin da ya ba ta saboda ta san yadda kungiyoyi masu zaman kansu suke yi, in suka bada irin wannan aiki, kuma suna biya bayan an kammala aikin.

Daga nan sai ta saki zuciyarta ta ci gaba da bin umurnin mutumin ta samo ma’aikata ta suka kwana suna aikin yin abinci.

Ta ce da suka kammala sai ta ƙira mutumin da nufin ta san waɗanda za su karɓi abincin, sai ya ce ta jira yana jiran a ba shi umurni tukuna.

“Bayan karfe 1 na rana ban ji ɗuriyarsa ba, sai na tafi ofishinsa, ya ce in jira yana jiran umarni.
“Bayan uku na yamma na fara ƙiran sa sau da yawa, amma ba ya ɗauka.

“Da muka je ofishinsa da mijina da misalin karfe biyar na yamma, sai aka ce mana ba ya nan.
“Tun daga lokacin ya ƙi ɗaukar wayata har ƙarfe biyar na yammaci.”

Hajiya A’isha ta ce ta yi matukar kaɗuwa da lamarin domin ta karɓi basussuka ne ta yi abincin.

Da ta kasa samun mutumin, sai ta shiga kafafen sada zumunta tana neman taimako.

Ta ce “Kwamishiniyar jin ƙai da bada agaji na Jihar Bauchj Hajiya Hajara Yakubu Wanka ta ƙira ni inda ta ce Gwamna ya ga bidiyona a intanet kuma ya umarce ta da ta biya ni diyya.

“Ina godiya ga Gwamna Bala Mohammed kan matakin da ya ɗauka na ceto ni cikin gaggawa.”
Hajiya Aisha ta ce gwamnati ta biya kuɗin da ta sayi kayan Naira miliyan 7.5 ba, kuma ta karɓi abincin aka rarraba shi wa masu bukata.

Da yake mayar da martani kan lamarin, babban sakatare a ma’aikatar, Alhaji Shuaibu Alhaji Muhammad, ya bayyana cewa asalin kuɗin kwangilar naira miliyan 13 ne, amma gwamnatin jihar ta biya diyya na ainihin kuɗin kayan abinci da Hajiya Aisha ta saya.

Wani abu daya ja hankalin jama’a shi ne Hajiya Aisha ta zabi kada ta bayyana sunan mutumin da ya yaudare ta, duk da cewa ta yi wa jami’an tsaro cikakken bayani.

Ta kuma gargaɗi jama’a game da masu zamba a asusun banki da za su ce za su rika neman tallafi da sunanta.

Kalli bidiyo a nan:

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like