No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Sani Gazas Chinade, Damaturu

Gwamnatin Jihar Yobe na shirin amincewa da bada tallafin  kimanin  naira dubu N35,000 ga ma’aikatan gwamnatin Jihar don rage raɗaɗin wahalhalun da cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi ke haifarwa ga rayuwar ma’aikatan da iyalen su.

Sakataren Gwamnatin jihar ya kasance shugaban kwamitin da gwamna Mai Mala ya naɗa don duba lamarin.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun muƙaddashin shugaban ma’aikatan jihar, Hamidu M. Alhaji, kuma aka mikawa sakataren gwamnatin jiha, Baba Malam Wali a jiya Juma’a a garin Damaturu.

Tun farko ne dai Gwamna Mai Mala Buni ya amince da naɗin sakataren Gwamnatin jihar Alhaji Bana Malam Wali a matsayin shugaban wannan  kwamitin kan bayar da tallafin naira dubu N35,000 ga ma’aikatan gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Buni ya ba da tallafin karatu ga ɗaliban koyon Shari’a kimanin 221 a Yobe

Sannan ya kuma bayyana cewa kwamitin na da mambobi shida tare da Babban Sakataren kula da ɓangaren ma’aikata a matsayin sakataren kwamitin.

Kwamitin zai tantance abin da ya shafi kuɗi na aiwatar da tallafin ga ma’aikatan da kuma yin shawarwari da ƙungiyoyin ƙwadago kan kuɗaɗen da za a amince da su a matsayin tallafin daga ɓangaren gwamnatin da kuma ƙungiyar ‘yan kwadago (NLC).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...