No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa

Gwamnatin Tarayya ta yi alƙawarin tallafa wa jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa da Naira biliyan uku domin rage musu raɗaɗin halin da suke ciki.

Ministan Kuɗi da Harkokin Tattalin Arziƙi, Mista Wale Edun ne, ya sanar da haka yayin wata ziyara da ya kai Jihar Kebbi.

Ya bayyana cewa kuɗin zai taimaka wa jihohi kamar Kebbi su taimaka wa manomansu don noman damina mai zuwa, wanda yake da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da wadatar abinci da kuma rage hauhawar farashin kayayyaki.

KU KUMA KARANTA: Mutum 129 sun mutu, sama da 120 suka jikkata sakamakon ambaliyar ruwa

Edun, ya kuma bayyana aniyar Shugaba Bola Tinubu na taimaka wa waɗannan jihohi don ci gaba da samar da tsaro da kuma haɓaka samar da abinci.

Ministan Kasafi da Tsare-Tsare, Sanata Atiku Bagudu, ya nuna damuwa game da ɓarnar da ambaliyar ta yi, amma ya yaba da ƙoƙarin mutanen Jihar Kebbi.

Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta tallafa musu don inganta noman damina.

Bugu da ƙari, Gwamnatin Tarayya ta amince da biyan kuɗi don aiwatar da ayyuka kamar hanyar Badagry zuwa Sakkwato da kuma faɗaɗa tsarin ban ruwa a kusa da hanyar, wadda za ta amfani Jihar Kebbi.

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya roƙi ƙarin tallafin Gwamnatin Tarayya, inda ya nuna damuwa kan lalacewar gonakin shinkafa.

Gwamna Idris ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta riga ta samar da kayayyaki ga manoma don taimaka musu game da noman damina.

Amma ya jaddada buƙatar taimakon Gwamnatin Tarayya saboda ƙalubalen da ambaliyar ruwa ta haifar a daminar bana.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...