No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Tarayya ta bai wa kowace jiha tirelar shinkafa 20

Gwamnatin Tarayya ta raba wa kowace jiha a Najeriya ciki har da Babban Birnin Tarayya, Abuja tirelar shinkafa 20 domin rage raɗaɗin ƙaracin abinci.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne, ya bayyana hakan bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya (FEC), na ranar Litinin.

Ministan, ya ce wannan shi ne mataki na farko da gwamnati ta ɗauka na magance matsalar ƙarancin abinci a ƙasar nan.

Ya kuma yi kira ga gwamnonin da su tabbatar an raba kayan ga marasa galihu a jihohinsu.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta fitar da wani rahoto da ya nuna hauhawar farashi ya ƙaru zuwa kashi 34.19 a watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya yaba da hukunci kotun ƙoli kan ƙananan hukumomi

NBS ta ce idan aka kwatanta da watanni baya, kayayyaki sun sake yin tashin gwauron zabi a Najeriya.

A gefe guda kuma ’yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan halin matsi da ake fama da shi, yayin da kuma matasa a ƙasar ke shirin tsunduma zanga-zanga a farkon wagan Agusta.

Sai dai batun shiga zanga-zangar ya haifar da cece-kuce da tada jijiyar wuyar tsakanin matasa da malamai a ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...