No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a, a matsayin ranar hutun Mauludi

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 5 ga Satumba, 2025 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

Wata sanarwa da babban sakatariyar ma’aikatar harkokin cikin gida, Dakta Magdalene Ajani ta fitar a madadin ministar, ta taya al’ummar Musulmin Nijeriya da ma wajenta murna, inda ta bukaci yin tunani a kan kyawawan dabi’un Manzon Allah na zaman lafiya, soyayya, tawali’u, juriya, da tausayi.

KU KUMA KARANTA: Islamiyoyi sama da 700 ne suka halarci zagayen Maulidin Annabi Muhammad (SAWW) a Potiskum

Sanarwar ta kuma yi kira ga ‘yan Najeriya na dukkan addinai da su yi amfani da wannan damar wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya, tsaro, da kwanciyar hankali, tare da marawa yunkurin gwamnati na hadin kai da ci gaba.

Ministan harkokin cikin gida yana yiwa al’ummar musulmi barka da Sallah lafiya.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...