No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Najeriya za ta ɗauki ma’aikatan lafiya dubu 28 da ke aiki ƙarƙashin USAID

Gwamnatin Najeriya ta sanarda aniyarta ta daukar ma’aikatan lafiya 28, 000 da hukumar raye kasashe ta Amurka (USAID) ke biya albashi, wacce shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da ayyukanta.

A hirarsa da wani shirin tashar talabijin ta Channels mai suna Hard Copy” na Juma’ar da ta gabata, ministan lafiyar Najeriya, Muhammad Ali Pate, ya bayyana cewar gwamnatin na tsare-tsaren zuke ma’aikatan lafiyan zuwa cikin tsarin kiwon kasar tare da rage dogaro akan tallafi daga kasashen ketare.

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar USAID ce ta ɗauki nauyin ƙungiyar Boko Haram – Ɗan Majalisar Dokokin Amurka

Ali Pate ya yabawa mahimmanci gudunmowar da gwamnatin amurka ke baiwa najeriya a fannin kiwon lafiya, musamman ma wajen yaki da cutar kanjamau da tarin fuka da kuma zazzabin cizon sauro.

Sai dai, ya jaddada aniyar Najeriyar na karbe iko da fannin lafiyarta tare da rage dogaro da tallafi daga ketare.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...