Labarai
Gwamnatin Najeriya ta yi ƙarin haske kan ziyarar da shugaba Tinubu zai kai Qatar
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/02/Tinubu-3.jpg)
Fadar shugaban Najeriya ta yi zargin cewa wasu mutane “masu muguwar aniya” ne suka fitar da wata wasiƙa game da ziyarar da shugaban ƙasar Bola Tinubu zai kai Qatar a watan gobe.
Wasiƙar, wadda aka yi musaya tsakanin ofishin jakadancin Qatar da ke Abuja da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya game da ziyarar kasuwanci da Shugaba Tinubu zai kai Qatar ranar 2 zuwa 3 ga watan Maris, ta jawo ce-ce-ku-ce ne bayan an yi zargin cewa gwamnatin Qatar ba ta so shugaban Najeriya ya je ƙasar.
Sai dai Bayo Onanuga, mai taimaka wa shugaban Najeriya kan watsa labarai da tsare-tsare, ya fitar da sanarwa da ke musanta cewa gwamnatin Qatar ba ta damu da ziyarar da Shugaba Tinubu zai kai ba.
KU KUMA KARANTA: Muna so shugaba Tinubu ya dawo da tallafin man fetur – Ƙungiyar ‘yan Arewa
“Muna masu sanar da cewa akwai dangantaka mai ƙarfi tsakanin ƙasashenmu biyu kuma muna so mu jaddada cewa Shugaba Bola Tinubu zai ziyarci Qatar ne bisa gayyatar da Sarkin Qatar, Mai Martaba Sheik Tamim Bin Hamad Al-Thani ya yi masa,” in ji Onanuga.
Kazalika wata sanarwa da Francisca Omayuli, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ta fitar ranar Asabar ta tabbatar da cewa Shugaba Tinubu zai ziyarci Qatar domin “ƙarfafa dangantaka mai gwaɓi da ke tsakanin ƙasashen biyu.”
Ziyarar za ta mayar da hankali wajen bunƙasa harkokin kasuwanci da diflomasiyya da sauransu, a cewar gwamnatin Najeriya.
Al'ajabi
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
![Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/building.jpg)
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.
Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.
An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.
KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja
Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.
Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.
Labarai
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
![Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/EFCC456.jpg)
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.
An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.
Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.
An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.
Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.
Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.
KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja
Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.
Labarai
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
![NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240701-WA0014-1-768x576-1.jpeg)
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.
Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.
A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.
Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .
Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.
KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J
Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.
Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.
A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano